Kotu Ta Daure Wani Mutum Wata 2 A Gidan Yari Kan Satar Doya
Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu. Wata Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya, Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin daurin watanni biyu a gidan yari bisa samunsa da laifin satar doya da darajarta ya kai Naira 144,000.
An yanke masa hukuncin ne kan laifin aikata laifuka da sata, amma ya roki kotun da ta yi masa sassauci. Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima’i A Benuwe. ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Sansanin Sojoji, Sun Kashe Dakaru 5 A Katsina. Alkalin kotun Jacinta Okeke, ta yanke wa Sani hukuncin zaman gidan yari na watanni biyu ko kuma yin aiki a kasuwar Gwagwalada.
Ta kuma gargade shi da ya guji aikata laifuka. Tun da farko, lauya mai shigar da kara, Abdullahi Tanko, ya shaida wa kotun cewa mai shigar da kara, Liasu Saidu, na kauyen Ukara, ya kai rahoton lamarin ofishin ‘yansanda a ranar 9 ga watan Mayu.
Labarai Masu Nasaba
Buga Kudi: EFCC Za Ta Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu A Ranar Laraba
Hajjin Bana: Gobe Maniyyata 428 Za Su Fara Tashi Daga Jihar Kebbi
Tanko, ya ce wanda aka yankewa laifin ya kutsa kai cikin gonar wanda ya kai karar ya tuge masa doyar da ya shuka wadda kudinta ya kai Naira 144,000. A cewarsa laifin ya sabawa sashe na 348 da na 287 na kundin laifuffuka.
إرسال تعليق