Posts

Turkashi: Yadda Whole Soyinka Ya Caccaki Shugaba Tunibu A Kan Yadada Yake Baiwa Dan Da Seyi.

Image
Frofesa Whole Soyenka Fittacen marubucin littafin Nobel ya Caccaki Tubibu yadda Ake Seye Dan sa Tsaro amma sauran mutane ba a damu dasu ba. Kamar yadda fa fada, ya ga “wani babbar rundunar tsaro ta kasa mai tarin yawa sosai da aka mallaka wa wani saurayi da ke da kusanci da Fadar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tunibu,” a wata rakiyar da ya bayyana a matsayin “wadda ta isa ta karɓe ƙaramar ƙasa gaba ɗaya.”  frofesa Whole Soyinka ya bayyana cewa daga baya sai ya fahimci cewa lallai wannan matashin Seyi Tinubu ne. “Nayi mamaki sosai kwarai da gaske matuƙar mamaki,” A cewarshi, sai Kuma ya ƙara da cewa “Lallai ya kamata yaro ya gane matsayin shi na yaro. Ba su ne Muka zaɓaba a matsayin shugabanni mu ba, kuma gaskiya yin hakan sam sam sai dace ba su gaji tsarin ikon mulki na ƙasa ba kawai saboda kusanci da mulki ba.”  A ra'ayina gaskiya yin hakan Bai kamata ba; inna fahimata ya Baiwa yaransa Tsaro amma yaran talakawa ba a damu dasu ba. Shin Al'umma yake wa aiki ko iyalansa da makusan...

Turkashi: Wani Matashi Yayi Tur Da Masu Yin Mummunan Kalamai Ga Sheik Dahiru Usman Bauchi.

Image
Wani Matashi Mai Suna Yusuf Sa'idu wanda akafi sani da Yusuf Senior dan garin Dogon-Dawa karamar hukumar Birnin-Gwari Kaduna state kuma dalibin jami'ar Ahmed Bello University (ABU) Zaria Ya Bayyana Cewa: Ya kamata mu dabi'antu da dayin adalci wa junanmu a mtasayin mu na musulmai w adanda ke annabi daya kur'ani daya, alkibla daya kar mubari son zuciya ya rufe mana idanuwa. Sheik Dahiru Usman Bauchi ya kasance shahararren babban malamin addinin musulunci kuma masoyin annabi Muhammad tsantsa ba Nigeria kadai ba Africa baki daya.  Ya sadaukar da rayuwarsa tun yana matshi baki daya wajan kiran mutane zuwa ga Allah da manzon Allah har zuwa lokacin da karfinsa ya Kare. Babban abunda ya ban mamaki wai ace musulmi zai iya zagin shehu! saboda me? Me shehu yayi masa? Ko da ma ace yayi masa wani abu na rashin kyautawa, ko bakomai ya kamata yaci arzikin musulunci, idan baici arzikin kasancewan shi kahdimul isalm, ko kuma yaci arzikin imimin sa, malintar sa, tsufar sa ko kuma '...

Da Dumu-Dumi: An Rantsar Da Musa Christopher A Matsayin Sabon Ministan Tsaro Na Kasa

Image
Babban jami'in tsaro Janar Christopher Musa (mai ritaya), tsohon babban hafsan hafsoshin tsaron Najeriya ya yi rantsuwar kama aiki a matsayin sabon ministan tsaron Najeriya a hukumance.  Majalisar dattijai ta tabbatar da nadin Musa a ranar Laraba bayan kammala tantance sa’o’i biyar da ‘yan majalisar suka yi.  A ranar Talata ne shugaban kasa, Bola Tinubu ne ya nada Musa, bayan murabus din da tsohon ministan tsaro, Badaru Mohammed ya yi, saboda matsalar lafiya. Ya himmatu wajen ba da fifiko ga tsaron lafiyar ‘yan kasa da kuma mutuncin yankin kasa. Domin samun sababbin labaran hauusa masu tushe da asali kuyi maza ku garzayo zuwa shfinmu mai suna EagleNewsHausa. Wanda ya ta nadar maku labaran gane Ilimi, addinin, Siyasa, Soyayya, sports da dukkaan abun da me faruwa a cikin gida Nigeria da Dmduniya baki daya.  

Innalillahi! 'Yan Bindiga Sunyi Wa Sojoji Mummunan Barna A Harin Da 'Yan Ta'addan Suka kai wa Sojoji

Image
 Wasu mahara dauke da makamai sun yi wa tawagar jami’an tsaron hadin gwiwa kwanton bauna a hanyar Kuzuntu da ke Anchau a karamar hukumar Kubau a jihar Kaduna, lamarin da ya yi sanadin mutuwar dan sanda guda tare da jikkata wasu sojoji da dama. A cewar sanarwar, tawagar jami’an tsaron da ta hada da jami’an sojin Najeriya, ‘yan sanda, ma’aikatan kiwon lafiyar dabbobi da ci gaban jihar Kaduna (KADVS) da kuma ‘yan banga na cikin gida, sun je wurin kiwo na gwamnati da ke Kuzuntu.  Sun yi rakiyar ma’aikatan wani kamfanin noma da kuma jami’an yankin domin tantance wuraren kiwo bisa bukatar shugaban karamar hukumar Kubau.  "Yayin da suka yi nasarar kammala aikin, an yi wa jami'an tsaro kwanton bauna a lokacin da suka dawo," in ji Makama.  An kashe dan sanda Sunday Ishaya a harin, kuma sojoji da dama sun samu raunuka. Domin samun sababbin labaran hauusa masu tushe da asali kuyi maza ku garzayo zuwa shfinmu mai suna EagleNewsHausa.   

Sunday Oliseh, Fitaccen Dan Wasan Super Eagles, Ya Tabbatar Da Cewa Real Madrid Na dia Sha'awar Siyan Victor Osimhen.

Image
Osimhen ya koma Galatasaray na dindindin a bazarar 2025 bayan ya shafe kakar wasa ta baya a matsayin aro.  Manyan kungiyoyin Turai da a baya suka yi watsi da shi yanzu sun gane gwanintarsa ​​a kakar wasa ta biyu. Ko da yake Oliseh ya tabbatar da zawarcin Real Madrid, bai bayyana majiyar bayanansa ba.  Osimhen ya kasance daya daga cikin ‘yan wasan gaba da ake nema ruwa a jallo a duniya tun lokacin da ya taka muhimmiyar rawa a nasarar da Napoli ta samu a gasar Seria A a kakar 2022/23.  Napoli ta hana shi yunkurin barin kungiyar a lokacin bazarar 2024, inda ya hana shi tafiya Saudi Arabiya mai riba tare da hana shi cimma yarjejeniya da Chelsea.

Yanzu-Yanzu: Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Christopher Musa A Matsayin Sabon Ministan Tsaron Nigeria.

Image
Majalisar dattijai ta tabbatar da Mista Musa a matsayin sabon ministan tsaron Najeriya bayan wani zaman tantancewa da ya kwashe kimanin sa'o'i uku ana yi a cikin kwamitin baki daya.  A ranar Laraba ne majalisar dattawa ta nada Christopher Musa, tsohon babban hafsan hafsoshin tsaro kuma Janar a matsayin a hukumance.  Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ne ya sanar da hakan bayan da ‘yan majalisar suka amince da wanda aka nada ta hanyar kada kuri’a a zaman kwamitin.  Tabbatar da hakan ya biyo bayan wani dogon nazari da ya shafi bangaren tambaya da amsa.  A yayin wannan zaman, Mista Musa ya nuna rashin amincewarsa da tattaunawa da ‘yan bindiga, ya kuma tabbatar wa ‘yan majalisar cewa, a karkashin shugabancinsa, ma’aikatar tsaro za ta kara himma wajen kawar da kungiyoyin masu aikata laifuka da ke barazana ga al’umma.  Ya kuma soki yadda ake mayar da tubabbun ‘yan Boko Haram cikin al’umma, yana mai cewa ya kamata ‘yan ta’adda su fuskanci hukunci mai tsauri. ...

Turkashi: Donald Trump Ya Dakatar Da Wasu Kasashen Zuwa Kasar Amuruka Ƙasashe, An Bayyana Dalilan.

Image
Shugaban Kasar Amuruka Donald Trump ya bada sanarwan cewa ya tsayar da shigan masu gudun hijira daga kasashe daban-daban Kimanin kasa goma saha tara (19), yana bayyana cewa baiwa Amuruka tsaron shine mafi komai muhimmanci a wajansa. Gwamnatin Amuruka ta saka Sababbin takunkumai wanda ya shafi hard masu neman Green Card da shaidar kasavcewa cikkaken 'yan kasar Amurka, wannan babban matakin ya samo asali ne Saboda Wani Mummunan Harin da wani ɗan Afghanistan ya kai wa sojojin Amurka a Washington, kuma laiial hakan yayi matukar harzuka Trump kan bakin kasar. Sabon labari : 'Yarn Ta'adda Sun Kai Dana ani mummunan harin a jihar Sokoto In Dai Suka yi Nasarar Sace amarya da ilahirin kawayen ta, a dai dai lokacin da ake tsaka da shan saha'anin bikin. @realDonaldTrump Source: Twitter Gwamnatin Donald Trump ta hana wasu Kasashen da dama, Kimanin 19 shiga kasar Amurka kamar Yadda USCIS tace. Domin samun sababbin labaran hausa masu tushe da asali kuyi maza ku garzayo zuwa shfi...