Posts

Showing posts from August, 2024

Muhimman Abu Buwan Da Yakamata Ku Sani Akan Sabuwar Mai Shari'ar Nigeria.

Image
Abin Da Ya Kamata Ku Sani Kan Sabuwar Babbar Mai Shari'a Ta Najeriya. Hukumar Shari'a ta Najeriya ce ta miƙa sunan Mai shari'a Kudirat Motonmori Kekere-Ekun ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu domin ya amince tare da naɗa ta a matsayin sabuwar Alƙaliyar Alƙalan Najeriya. A ranar Juma'a ake sa ran shugaban ƙasar zai naɗa ta a fadarsa da ke Abuja. Kakakin hukumar, Soji Oye ya ce hukumar NJC ta amince da matakin ne a zamanta wanda Babban mai shari'a na Najeriya mai barin gado, Olukayode Ariwoola ya jagoranta. "Wannan yana da muhimmanci sosai kasancewar shekarun ajiye aiki na Mai shari'a Olukayode Ariwoola sun cika ne a ranar Alhamis 22 ga Agustan 2024." Olukayode Ariwoola ya yi riƙe matsayin ne tun daga ranar 21 ga watan Satumban shekara ta 2022, zamanin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari. 'Dole a yi gyara a bangaren shari’a ta Nijeriya ' 28 Nuwamba 2023. A bu 10 kan sabon Alkalin Alkalan Najeriya27 Yuni 2022.  Masu jiran a zartar musu da hukuncin kis...

Inalillahi! 'Yan Bindiga Sun Kashe Sarkin Gubir A Sokoto.

Image
' Yan bindiga sun kashe Sarkin Gobir Isa Bawa bayan garkuwa da shi. Bayanan hoto,Mako uku kenan bayan 'yan bindigar sun sace sarkin a kan hanyarsa ta komawa gida Rahotannin da muke samu daga jihar Sokoto na cewa ƴan bindigar da suka yi garkuwa da Sarkin Gobir na garin Gatawa, Alhaji Isa Bawa, sun kashe shi. A cikin wannan makon ne sarkin ya fito a wani bidiyo yana neman gwamnatin jihar Sokoto ta biya 'yan bindigar kudin fansa da suka bukata, inda ya ce idan wa'adi ya cika ba a biya ba za su halaka shi. Mako uku da suka wuce ne 'yan bindiga suka yi garkuwa da sarkin a yankin kwanar maharba lokacin da yake kan hanya bayan halartar wani taro a cikin garin Sokoto.

Da Ɗumi-Ɗumi: Gwamnonin Nigeria Sun Amince Da Tsarin Mulikin Tunibu.

Image
Gwamnonin Nijeriya Sun Aminta Da Salon Mulkin Tinubu. Majalisar koli ta kasa da kungiyar gwamnonin Nijeriya, sun jaddada amincewarsu ga salon shugabancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Gwamnan Jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazak, wanda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin, ya shaida hakan ga manema labarai a ranar Talata jim kadan bayan ganawa daban-daban da bangarorin biyu suka yi da shugaba Tinubu. Nijeriya Ta Fara Sayar Da Makaman Da Ta Ke Kerawa – Minista Nazarin CGTN Ya Bayyana Yadda Wasu Mutanen Duniya Suka Soki EU Game Da Takkadamar Cinikayya Tsakaninta Da Sin Wannan na zuwa ne kwanaki bayan zanga-zangar adawa da yunwa da matsin rayuwa a kasar. Majalisar kolin dai, ta kunshi tsofaffin shugabannin Nijeriya, zababbu da na mulkin soja, da gwamnoni, da ministoci, da shugabannin majalisar tarayya wanda suka gana da shugaban Tinubu. Daga bisani kungiyar gwamnoni ta yi nata ganawar, inda suke tattauna halin da kasa ke ciki da kuma matakan da ya kamata a dauka. Labarai Masu Nasaba Albashin Da ...

Yanzu-Yanzu: Hukumar Ƙarshe Gobara Ta Kano Ta Ceto Mutane 154 Da Kadarorin Naira Mikyan 8.

Image
Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Mutum 154 Da Kadarorin Naira Miliyan 80 A Watan Yuli. Hukumar kashe gobara Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce ta ceci mutane 154 da kadarori da darajar kuɗinsu ya kai naira miliyan 80 daga aukuwar gobara 13 daban-daban a watan Yuli. Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar Alhaji Saminu Abdullahi, ne ya bayyana hakan cikin wata hira da ya yi da manema labarai yau Litinin a Kano. NIS Ta Fara Binciken Wata Mata Da Ta Yayyaga Fasfonta A Filin Jiragen Sama Na Legas Kungiyar NLC Ta Nemi Rundunar ‘Yan sanda Ta Nemi Afuwarta  Abdullahi, ya ce duk da wannan namijin ƙoƙari kimanin mutum 150 da dabbobi da dama sun mutu sakamakon gobarar da aka yi a tsawon lokacin, bisa yadda aka yi nazari a kai yayin da kuma gobara ta lalata dukiya da ta kai darajar naira miliyan 27. Labarai Masu Nasaba An Yi Asara Kimanin Naira Biliyan 500 Sakamakon Zanga-zanga – Minista Gwamna Bago Ya Yi Allah-wadai Da Kona Coci A Neja. Ya shawarci jama’a da su riƙa kula da wuta tare da...

Inalillahi! Wata Mata Ta Zubar Da Cikin Wata Tara .

Image
'Yan Sanda Na Binciken Matar Da Ta Zubar Da Cikin Wata Tara. 'Yan sanda a Koriya ta Kudu na bincikar matar da ta zubar da cikinta ya na wata tara.  Matar ta yi bayani a kan yadda ta zubar da cikin nata dalla-dalla a wani bidiyo da ta wallafa a shafinta na sada zumunta, lamarin da ya fusata mutane aka rika mayar mata da martani. Dokar zubar da ciki ta kasar dai ta gama aiki tun shekaru uku da suka gabata, ma'ana yanzu ba a san takaimaimai hukuncin zubar da ciki ba. A yanzu 'yansandan na kokarin ganin ko za su gurfanar da ita gaban kuliya da ma likitan da ya zubar mata da kisan kai.