Posts

Showing posts from October, 2024

Turƙashi: Manufar Shugaba Bola Tunibu Ga 'Yan Nigeria

Image
' Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Manufar Gwamnatin Tinubu ' Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya  ta shaidawa babbar jam'iyyar adawar kasar, ba gudu ba ja da baya kan manufofin da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sanya a gaba, za kuma su ci gaba da goyon bayan shi kan farfado da kyakkyawan fatan 'yan Najeriya. Jaridar Daily Trust ta rawaito APC na nanatawa PDP babu wani magudi da aka yia zaben gwamna da aka yi a jihar Edo makonnin da suka gabata, wanda jam'iyyar PDP ami mulki ta sha kaye a zaben da aka yi. Jam'iyyar ta yi watsi da jita-jitar gwamnatinsu na son maida siyasar kasar ta jam'iyya daya, da salon mulkin kama karya. Daily Trust ta ce a ranar Alhamis ne dai kwamitin amintattun jam'iyyar adawa ta PDP, ya zargi APC da kulla mkarkashiya a zaben da aka yi na jihar Edo, Da ya ke jawabi ga manema labarai bayan taron na kwamitin amintattu, shugaban kwamitin, Sanata Adolphus Wabara, ya bayyana damuwa kan yadda lamura ke kara tabarbarewa a Najeriya mus...

Da Dumi-Dumi: Hotunan Ɓarnar DA Isra'ila Suka Yi A Daren Jiya A Lebanon.

Image
Hotunan Ɓarnar Da -Haren-Haren Isra'ila Suka Yi A Daren Jiya A Lebanon. Hare-haren da Isra'ila ta kai cikin daren jiya a Lebanon ya kashe mutum 22 tare da jikkata sama da 100. Ga wasu daga cikin hotunan ɓarnar da hare-haren suka yi a birnin Beirut.

Yanzu-Yanzu: Sarkin Musulmi Yayi Kira Da Adaina Zagin Shugabanni

Image
  Sultan Ya Buƙaci Ƴan Najeriya Su Daina Tsine Wa Shugabanni Mai alfarma Sarkin Sokoto, Alhaji Sa'ad Abubakar III ya yi kira ga ƴan Najeriya da cewa da su riƙa yi wa shugabannin ƙasar addu'a duk yanayin da ake ciki, kuma duk yanayin da ƙasar ke ciki. Sultan ya yi wannan kiran ne a Jami'ar Ilorin a ranar Alhamis a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron ƙaddamar da littafin da aka rubuta a kan shugaban hukumar JAMB Farfesa Is’haq Oloyede, wanda ya yi ritaya daga aikin jami'a kamar yadda Daily Trust ta ruwaito. Sultan ɗin ya ƙara cewa, "ku daina tsine wa shugabanni duk yadda abubuwa suka lalace, maimakon haka gara ku riƙa musu addu'a.  Ku daina faɗin abubuwa marasa kyau a kansu. Duk lalacewar shugaba ku guji tsine masa," in ji shi. A nasa jawabin, ministan shari'a Lateef Fagbemi (SAN), wanda shi ne shugaban taron, kira ya yi ga ƴan Najeriya da su riƙa ƙarfafa wa shugabanninsu gwiwa. "Ban ce babu matsala ba, amma da zarar kun fara ɓata ƙasarku a id...

Da Dumi-Dumi: Farashin Gidajen Man NNPCL Yayi Tashin Kwan Zabo

Image
Sabon Farashin Litar Mai A Gidajen Man NNPCL Ya koma N1,030 A Abuja.   Aminu Kutama ya yi zuwa wasu gidajen mai mallakar kamfanin mai na Najeriya, NNPCL a Abuja ya nuna yadda ake sayar da man a kan sabon farashi na naira 1,030 kowacce lita saɓanin yadda ake sayar da shi a baya naira 897 kowacce lita. Ƙarin na kimanin kaso 15, shi ne na biyu a tsawon wata guda. Wannan dai na zuwa ne bayan bayanan da suka nuna kamfanin na NNPCL ya zare hannunsa daga dillancin man kamfanin Ɗangote, wani abu da ya nuna cewa akwai yiwuwar farashin man ya ƙara tashi. Zare hannun NNPCL daga dillanci dai na nufin kamfanin ya daina cikasa giɓin da ake samu ko kuma tallafi na naira 133.  Aminu Kutama ya ce daga zagayen da ya yi a Abuja cewa ana sayar da man a wasu gidajen man ƴankasuwa daga naira 1,040 zuwa sama. Wane tasiri zare hannun NNPCL daga dillancin man Dangote zai yi ga ƴan Najeriya? 8 Oktoba 2024 Tarihin ƙarin farashin man fetur a Najeriya daga shekarar 2000-2024 9 Satumba 2024 Ko ƙarin farash...

Yanzu-Yanzu: Red Bull Ta Bai Wa Klopp Aikin Shugaban Ƙwallon Kafar Ƙungiyar.

Image
Red Bull Ta Bai Wa Klopp Aikin Shugaban Ƙwallon Kafar Ƙungiyar. Red Bull ta naɗa tsohon kociyan Liverpool, Jurgen Klopp a matakin shugaban ƙwallon kafar ƙungiyar. Mai shekara 57 ɗan kasar Jamus, zai fara aiki ranar 1 ga watan Janairun 2025. Kamfanin Red Bull shi ne ya mallaki RB Leipzig a Jamus, mai buga Bundesliga da Red Bull Salzburg ta Australia da New York Red Bull mai buga gasar Amurka ta Major League Soccer da ƙungiyar Red Bull Bragantino ta Brazil. Haka kuma Red Bull yana da hannun jari a Leeds United mai buga Championship, ya kuma kulla yarjejeniyar sa tallan kamfanin a rigar ƙungiyar a farkon shekarar nan.  Red Bull ya ce Klopp ba zai sa hannu a gudanar da aikin yau da gobe ba, amma zai ke bayar da shawara kan yadda za a samu ci gaba da bunkasa wasannin ƙungiyar da masu horar da ita. Klopp ya lashe kofi takwas a kaka tara a Liverpool, ciki har da Premier League da Champions League, wanda ya ajiye aikin a karshen kakar da ta wuce.  Ya fara aikin horar da tamaula a Main...

Da Dumi-Dumi: Gwamnati Ta Cire Tallafin Aikin Hajji.

Image
Gwamnati Ba Za Ta Ci Gaba Da Biyan Tallafin Aikin Hajji Ba – NAHCON Hukumar aikin Hajji ta kasa (NAHCON), ta sanar da cewa gwamnatin tarayya ba za ta iya ci gaba da biyan tallafi aikin hajjin ba kamar yadda ta saba ta hanyar karyar wa maniyyata farashin dala a babban bankin ƙasar nan CBN. Mai magana da yawun hukumar, Fatima Sanda Usara, ce ta shaida haka cikin wata sanarwa da ta fitar, inda ta ce gwamnati ta daina bai wa maniyyata tallafin rangwamen farashin dala a jihohi da tarayya.  Muna Tattaunawa Don Ganin An Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya – Kamala Harris Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina – Ibrahim Masari  Tuni dai masana harkokin aikin Hajji a Nijeriya suka fara tsokaci game da yadda aikin hajjin baɗi na 2025 zai kasance sakamakon cire hannun gwamnati daga wanda suka yi hasashen kuɗin aikin Hajjin 2025 ka iya kai wa miliyan 10 ko fiye. Sun bayyana cewa idan aka tafi a haka yadda farashin dala je tashin gwauron zabi, a yanz...

Yanzu-Yanzu: Ecowas Zata Samar Da Rundunar Dakaru 5,000 Don kawo Ƙarshe Ta'addaci

Image
  Ecowas Za Ta Samar Da Runduna Ta Dakaru 5,000 Don Yaki Da Ta'addanci Ƙungiyar Ecowas ta ce tana shirin kafa runduna ta dakaru 5,000 domin yakar ta'addanci a yankinta na yammacin Afrika.  Shugaban hukumar Ecowas Omar Touray wanda ya bayyana haka a wani taron tsaro da aka gudanar a Abuja ya ce an kai hare-hare 1,605 tsakanin watan Janairu zuwa Agustan 2024 a yammacin Afirka, kuma an samu hasarar rayuka 6,956. Ya ce, "bisa umarnin shugabannin ƙasashen Ecowas, akwai yunƙuri da ake na samar da runduna ta dakaru 5,000 domin yaƙi da ta'addanci."  Mali da Burkina Faso da Niger da Nigeria ne ƙasashen da matsalar tsaro ta fi addaba a yankin. Mista Touray, ya ce a Burkina Faso an kai hare-hare 611 attacks inda aka kashe mutum 3,810. A Mali na kai hare-hare 546 inda aka kashe mutum 1424.  A Najeriya kuma an kai hare-hare 238 yayin da kuma aka kashe mutum 905, sai Nijar inda aka kai hare-hare153 tare da samun hasarar rayuka 676.  An kuma kai hare-hare 44 a Benin da hasarar...

Da Dumi-Dumi: Gwamna Zulum Ya Hana Gini A Magudanar Ruwa.

Image
Gwamna Zulum Ya Hana Gine-Gine A Magudanar Ruwa. Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum ya bayyana takaicinsa a kan yadda mutane suke gina gidaje a magudanar ruwa a jihar.  Zulum ya bayyana haka ne a ranar Alhamis bayan ya kai ziyarar duba ɓarnar da ambaliyar - wadda ta ɗaiɗaita jihar - ta yi ga hanyoyin mota da gadoji da asibitoci da sauransu. A cewarsa, "Ɓarnar ta yi yawa. Mun ziyarci wurare da dama mun gani. Akwai ban takaici yadda mutane suke gina gidaje a magudanar ruwa.  Ba don a tare masa hanya ba, da ruwan zai riƙa bin hanyarsa yana wucewa ne. "Duk da gargaɗin da ake yi, amma har yanzu mutane suna cigaba da gini a magudanar ruwa, wanda irin waɗannan matsalolin ne suka jawo ambaliyar.  Ba za mu watsar da kula da rayuwar mutanen Maiduguri ba saboda wasu ɗaiɗaikun mutane," in jij shi kamar yadda Daily Trust ta ruwaito. A ƙarshe ya yi kira ga ma'aikatar aikace-aikace da jami'an tsaro su tabbatar babu wanda ya sake yin gini a magudanar ruwa a jihar

Wata Sabuwa: Mbappe Ba Zai Samu Buga Ma Faransa Nastions League Ba

Image
Mbappe Ba Zai Buga Wa Faransa Nations League Ba. Kylian Mbappe ba zai buga wa Faransa Nations League ba, duk da ya murmure daga raunin da ya yi jinya.   Bai yiwa Real Madrid wasan da ta tashi 1-1 ba da Atletico Madrid ranar Lahadi, amma ya buga karawar da Lille ta ci Real 1-0 a Champions League ranar Laraba. Duk da ya buga wa Real Madrid gasar zakarun Turai, amma Didier Deschamps bai gayyace shi wasan da zai fuskanci Israel da Belgium ba. Mbappe ya ci ƙwallo bakwai a wasa 10 tun bayan da ya koma Real Madrid a bana daga Paris St Germain.  Haka shima Antoine Griezmann ba zai buga karawar ba a karon farko, wanda ya sanar da yin ritaya ranar Litinin. Mai shekara 33 ya buga wa Faransa wasa 137 da lashe kofin duniya a Rasha a 2018 da kai wa wasan karshe a Qatar a 2022.  Christopher Nkunku, wanda ya buga wa Faransa wasa na 10 a watan Yuni, yana cikin waɗanda aka gayyata, amma banda N'Golo Kante. Faransa za ta fara ziyartar Israel ranar Alhamis 10 ga watan Oktoba a Budapest daga ...

Yanzu-Yanzu: Zanga-Zanga Ta Ɓarke A Ƙasar Ghana

Image
Matasa Sun Sake Fita Zanga-Zanga Domin Neman A Saki Ƴan Uwansu A Ƙasar Ghana. Ƙungiyoyin matasa a Ghana sun hau kan titunan biranen ƙasar domin yin zanga-zangar neman a saki masu zanga-zanga 50 da wata kotu ta bai wa ƴan sanda damar tsare su a makon da ya gabata. Wata zanga-zangar kwana uku ta nuna ƙin amince wa da haƙar ma'adanai a ƙasar ba bisa ka'ida ba ta janyo arangama tsakanin masu zanga-zangar da jami'an tsaro al'amarin da ya janyo akakama masu zanga-zangar da dama bisa tuhumar haɗuwa ba bisa ƙa'ida ba. Da safiyar Alhamis ne kuma ɗaruruwan masu zanga-zangar suka yi dafifi inda suka hau titunan birnin Accra suna neman a saki mutum 50 ɗin da ake tsare da su. Mutanen ƙasar da dama dai sun alawadai da abin da ƴansandan da kotu suka yi na tsare matasan har tsawon makonni biyu. Ƙasar Ghana dai ita ce wadda ta fi kowacce ƙasa albarkatun gwal a nahiyar Afirka, to sai dai ƙasar tana fama da matsalar haƙar ma'adan ba bisa ƙa'ida ba wani al'amari da ya jawo ...

Da Dumi-Dumi: Atiku Ya Buƙaci A Mai Da Mulkin Najeriya Na Karɓa-karɓa

Image
Atiku Ya Buƙaci A Mayar Da Mulkin Najeriya Na Karɓa-karɓa. Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira da a yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar garambawul domin mayar da mulkin ƙasar na karɓa-karɓa a tsakanin yankunan ƙasar guda shida. Atiku, wanda shi ne ɗantakarar PDP a zaɓen shugaban ƙasa da aka yi bara ya kuma yi kira da a mayar da shugabancin ƙasar ya zama zango ɗaya na shekara shida maimakon zango biyu na shekara huɗu-huɗu. Atiku ya aike da buƙatar hakan ne ga kwamitin gyara kundin tsarin mulkin ƙasar na Majalisar Dattawa, wanda ya fara zama domin yi wa kundin na 1999 garambawul ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa sanata Barau I. Jibrin, kamar yadda muka kalato daga jaridar Daily Trust. Haka kuma ya buƙaci a yi gyara a ɓangaren mafi ƙarancin matakin karatun masu neman shugabanci, da sauransu.

Innalillahi! kwale-kwale Ya Kife Da Mutane Fiye Da 250 A Jihar Naija.

Image
Yadda kwale-kwale Ya kife da Masu Mauludi 300 A Jihar Naija. Wata sanarwa da kakakin hukumar agajin gaggawa ta jihar, Abdullahi Baba Arah ya fitar, ta ce akwai sama da fasinjoji 300 a cikin kwale-kwalen lokacin da ya kife a madatsar ruwa ta Jebba a garin Gbajibo da ke ƙaramar hukumar da yammacin ranar Talata. Abdullahi Arah ya ce kwale-kwalen wanda ya taso daga Mundi zai tafi Gbajibo domin halartar bikin Maulidi cike yake maƙil da mata da ƙananan yara. Kakakin hukumar ta agajin gaggawa ta jihar ya ƙara da cewa yanzu an ceto mutum fiye da 150 da ransu. Sai dai wata sanarwa da shugaban ƙaramar hukumar ya fitar da gidan talbijin na Channels ya rawaito ta nuna cewa aƙalla gawarwaki 60 ne aka gano sannan kuma ana ci gaba da neman wasu daga cikin fasinjojin. Sanarwar ta ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan ceto ƙarƙashin jagorancin hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar da sauran mutane. Ko a watan Satumban 2023, an samu kwatankwacin irin wannan, inda kwale-kwale ɗauke da fasinja...

Wata Sabuwa: "Na Ranstse Da Qurani Ban Saci Kudin Kaduna Ba" Nasiru El-Rufa-ee

Image
Zan Iya Rantsewa Da Ƙur'ani Ban Saci Kuɗin Kaduna Ba - El-Rufai. Tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya ce zai iya rantsewa da Ƙur'ani bai saci kuɗi ba a lokacin da yake mulkin jihar. Ya bayyana hakan ne a wani shiri na gidan rediyon Freedom da ke Kaduna a ranar Talata kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito. Majalisar Jihar Kaduna dai tana binciken tsohon gwamnan ne bisa zargin karkatar da sama da naira biliyan 324 a zamaninsa, zargin da tsohon gwamnan da waɗanda suka aiki tare suka ƙaryata. A cewarsa, "Na yi shiru ne domin ganin yadda za ta kaya. Ina yawan addu'ar Allah Ya min jagora a duk abin da nake yi a rayuwa.   A matsayina na ɗan Adam, ina ƙoƙari wajen guje wa cin amanar mutane ko kuma aikata wani abu da bai dace ba. "Na sha faɗa cewa duk lokacin da tsofaffin gwamnonin Kaduna da sauran shugabanni suka yarda a yi rantsuwa da Ƙur'ani cewa ba su saci kuɗin al'umma ba, to nima a shirye nake saboda na san ban shiga siyasa domin sata ba.  Na sh...

Yanzu-Yanzu: Shugaban Iran Yayi Gargaɗi Ga Isra'ila.

Image
Shugaban Iran Yayi Gargaɗi Ga Isra'ila. Shugaban Iran Massoud Pezeshkian ya kare matakin harin da ƙasarsa ta kai tare da yin gargaɗi ga Isra'ila. A shafinsa na X, shugaban ya ce "bisa la'akari da haƙƙin Iran tare da manufar zaman lafiya da tsaron Iran da yankin, an mayar da martani ga Isra'ila don kare muradun Iran da ƴan ƙasa." Da ambaci Netanyahu, inda ya ce Firaministan Isra'ila ya sani cewa "Iran ba mayyar yaƙi ba ce, amma za ta kare kanta daga duk wata barazana. Ya yi gargaɗi ga Isra'ila cewa wannan harin kamar kyaftawar ido ne" na ƙarfin Iran da kuma kaucewa shiga yaƙi da Iran.. Wannan na zuwa yayin da rundunar sojin Isra'ila ta ce za ta ƙaddamar da harin martani cikin gaggawa ba tare da ɓata lokaci ba.