Da Dumi-Dumi: Atiku Ya Buƙaci A Mai Da Mulkin Najeriya Na Karɓa-karɓa

Atiku Ya Buƙaci A Mayar Da Mulkin Najeriya Na Karɓa-karɓa.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira da a yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar garambawul domin mayar da mulkin ƙasar na karɓa-karɓa a tsakanin yankunan ƙasar guda shida.

Atiku, wanda shi ne ɗantakarar PDP a zaɓen shugaban ƙasa da aka yi bara ya kuma yi kira da a mayar da shugabancin ƙasar ya zama zango ɗaya na shekara shida maimakon zango biyu na shekara huɗu-huɗu.

Atiku ya aike da buƙatar hakan ne ga kwamitin gyara kundin tsarin mulkin ƙasar na Majalisar Dattawa, wanda ya fara zama domin yi wa kundin na 1999 garambawul ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa sanata Barau I. Jibrin, kamar yadda muka kalato daga jaridar Daily Trust.

Haka kuma ya buƙaci a yi gyara a ɓangaren mafi ƙarancin matakin karatun masu neman shugabanci, da sauransu.

Comments

Popular posts from this blog

Yanzu-Yanzu: Babbar kotun koli Ta Kasa Nigeria Ta Umarci Jam'iyyar PDP Ta Bai wa Tsohon Gwamnan Jigawa Daman Fitowa Takarar Shugabanci Jam'iyyar.

Abun-Mamaki: Wajen Jana'izar Sheik Dahiru Usman Bauchi /Sababbin kabarai na hausa EagleNewsHausa

Ana Wata Ga Wata: 'Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Mata 12.