Yanzu-Yanzu: 'Yan Sanda Sun Ceto Mutum 3 Daga Wani Gini Da Yarushe A Abuja .

An Ceto Mutane 3 Daga Wani Gini Da Ya Rushe A Abuja – ‘Yansanda.

Rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya, Abuja, ta tabbatar da rushewar wani gini mai hawa hudu ne a yankin Garki.

Sanarwar da kakakin rundunar, SP Josephine Adeh, ta fitar ta ce ginin ya rushe ne ranar Litinin da daddare.

Mutane 20 Sun Mutu, 52 Sun Ji Rauni A Harin Bam A Borno – DHQ

Kwastam Ta Kama Bindigu A Tashar Jiragen Ruwa A Ribas

Ta ce bayan samun kiran waya kan lamarin, kwamishinan ‘yansandan Abuja, Benneth Igweh, ya tura jami’ansa zuwa wurin.

A cewar sanarwar, an kubutar da mutum uku daga cikin ginin da ya rushe, inda kuma aka garzaya da su asibiti domin samun kulawa da lafiyarsu.

Sanarwar ta bayyana cewa rundunar ta ankarar da hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa domin su ɗauki ragamar zaƙulo mutanen da ƙasa ta birne.

Labarai Masu Nasaba

Mutane 20 Sun Mutu, 52 Sun Ji Rauni A Harin Bam A Borno – DHQ. Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniyar Yakar Yunwa Da Saudiyya


Rundunar ‘yan sandan ta kara da cewa an sanar da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) da Hukumar Kula da Ci gaban Kasa ta Babban Birnin Tarayya Abuja, kuma jami’ansu sun wajen domin gudanar da nasu aikin.

Comments

Popular posts from this blog

Yanzu-Yanzu: Babbar kotun koli Ta Kasa Nigeria Ta Umarci Jam'iyyar PDP Ta Bai wa Tsohon Gwamnan Jigawa Daman Fitowa Takarar Shugabanci Jam'iyyar.

Abun-Mamaki: Wajen Jana'izar Sheik Dahiru Usman Bauchi /Sababbin kabarai na hausa EagleNewsHausa

Ana Wata Ga Wata: 'Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Mata 12.