Da Dumi-Dumi: Rikici Ya Ɓarke Tsakanin Fulani Da Manoma.
Fadan Fulani Da Manoma Ya Ɓarke A Jigawa, An Samu Asarar Rayukan A Yau Asabar.
faɗan Fulani da manoma da ya ɓarke a ƙaramar hukumar Miga ta jihar Jigawa ya jawo asarar rayukan mutum tara Wasu mutum huɗu kuma sun jikkata bayan da faɗan ya ɓarke a safiyar ranar Juma'a, 3 ga watan Janairun 2025 Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta hannun kakakinta, ta tabbatar da aukuwar lamarin mara daɗin ji.
Jihar Jigawa - An samu tashin hankali tsakanin makiyaya da manoma a jihar Jigawa. Faɗan makiyayan da manoman dai ya auku ne a ƙauyen Gululu, da ke a ƙaramar hukumar Miga da ke jihar Jigawa.
Yadda rikicin ya auku Jaridar Tribune ta rahoto cewa Magajin Garin Gululu, Malam Muhammad Sarkin-Dori, ya ce lamarin ya auku ne a ranar Juma'a da safe.


Comments
Post a Comment