Inalillahi! Allah Yayi Wa Babban Malamin Musulunci Rasuwa.
Babban Malamin Musulunci Ya Rasu A Gombe, Farfesa Pantami Ya Magantu.
Tsohon Ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami ya yi ta'aziyyar rasuwar fitaccen malamin Musulunci a jihar Gombe Pantami ya tura sakon ta'aziyya ga iyalan marigayin, Sarkin Malaman Funakaye.
Malam Adamu Abubakar Bajoga Marigayin ya rasu ne a ranar Lahadi 5 ga watan Janairun 2025 wanda aka gudanar da jana'izarsa a safiyar Litinin 6 ga watan Janairun 2025
Bajoga, Gombe - An shiga alhini bayan sanar da rasuwar fitaccen malamin Musulunci a jihar Gombe, Malam Adamu Abubakar Bajoga.
Marigayin ya rasa ransa ne a ranar Lahadi 5 ga watan Janairun 2025 inda aka yi jana'izarsa a safiyar ranar Litinin a garin Bajoga da ke jihar Gombe.
Gombe: An yi jana'izar babban malamin Musulunci Tsohon Ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami ya mika sakon ta'aziyyarsa a gajeren rubutu da ya yi a sha

Comments
Post a Comment