Innalillahi! Wasu Matasa Sun Kona Wani Mutum Har Lahira
Zargin Maita': Wasu Fusatattun Matasa Sun Bankawa Ɗan Najeriya Wuta Har Lahira.
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kama mutane 17 da ake zargi da kashe wani mutumi a jihar Ebonyi, bisa zargin yana maita An zargi Uromchi Okorocha, da zama silar mutuwar wasu mutane ta hanyar lashe kurwarsu.
Alamarin da ya jawo aka kona shi Sufeto janar na ‘yan sanda ya yi Allah wadai da masu daukar doka a hannu, yana kira ga al’umma su rika kai rahoto ga hukumomi
Rundunar ‘yan sanda a jihar Ebonyi da ke Kudu maso Gabas ta kama mutane 17 da ake zargi da kona wani mutum bisa zargin maita.
Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Lahadi, inda ya ce lamarin ya faru a ranar 3 ga Janairu.

Comments
Post a Comment