Turkashi! Koriya Tace Baza Ta Bar Ƙera Makaman Nukiliya Ba

Baza Mu Daina Ƙera Makaman Nukiliya Ba - Kim Jong Un. 

Shugaba Kim Jong Un na Koriya ta Arewa ya sha alwashin ci gaba da shirin kasar na kera makaman nukiliya har sai baba ta gani.

Kafar yada labaran ƙasar ta rawaito Mr Kim ya kai ziyara cibiyar da ake kera makaman, inda ya ce shekarar da muke ciki na da matuƙar muhimmanci a tsarin da ƙasar ke yi na ƙarfafa shirin makaman nukiliya, da kuma fito na fito da duk ƙasashen da suka nemi tsoma baki a harkar ƙasarsa.

Kalaman Kim na zuwa ne bayan gwajin makaman da Pyongyang ta yi a ranar Asabar da ta wuce, domin tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro, shi ne gwaji na farko tun bayan shugaban Amurka Donald Trumo ya sha rantsuwar kama aiki.

A ɓangare guda kuma Mr Trump ya ce zai sabunta hulɗar da ke tsakaninsa da shugaban na Koriya ta Arewa.

Comments

Popular posts from this blog

Yanzu-Yanzu: Babbar kotun koli Ta Kasa Nigeria Ta Umarci Jam'iyyar PDP Ta Bai wa Tsohon Gwamnan Jigawa Daman Fitowa Takarar Shugabanci Jam'iyyar.

Abun-Mamaki: Wajen Jana'izar Sheik Dahiru Usman Bauchi /Sababbin kabarai na hausa EagleNewsHausa

Ana Wata Ga Wata: 'Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Mata 12.