Turkashi! kujerar Shugaba Tunibu Ta Fara Rawa
Matasa Sun Ajiye Tinubu, Sun Fara Kiran Rahama Sadau Ta Fito Takarar Shugabar Kasa.
Wani matashi ya bukaci 'yar wasar fim, Rahama Sadau ta fito takarar shugabar Najeriya a 2027 domin shahararta da tarin masoya Wasu sun goyi bayan wannan kiran yayin da wasu suka nuna ko kusa ba ta cancaci neman kujerar Shugaba Bola Tinubu ba.
Wannan na zuwa ne yayin da Rahama ta wallafa "Salaam" a soshiyal midiya, wanda ya sa mutane sama da 2,200 suka yi martani
Kaduna - Soshiyal midiya ta dauki zafi da wani matashi ya nemi fitacciyar jarumar Kannywood, Rahama Sadau ta fito takarar shugabar Najeriya a 2027.
An nemi Rahama Sadau ta gwabza da Shugaba Bola Tinubu a 2027 ne yayin da jarumar ta wallafa wani sako da ya ja hankalin dubunnan mutane.

Comments
Post a Comment