Yanzu-Ynazu: Israela Ta Kashe Fasdinawa Goma(10)

Ma'aikatar Lafiyar Hamas Tace Isra'ila Ta Kashe Falasɗinawa 10.

Ma'aikatar lafiya a Falasɗinu ta ce hari ta sama da Isra'ila ta kai yamma da gaɓar kogin Jordan da ta mamaye ya hallaka aƙalla Falasɗinawa 10.

An kai harin ne a yankunan Tunbas da Samaria da ke arewacin kogin Jordan.

Wakilin BBC ya ce ƴan makonnin nan Isra'ila ta zafafa kai hare-haren soji a arewacin yamma da gaɓar Kogin Jordan musamman a Jenin, inda hukumomin Falasɗinu suka gwabza faɗa da Hamas da mayaƙan jihadi.

Hotunan bidiyo da ake kyautata zaton a garin Tamoun ne, ya nuna yadda mutane suka cika maƙil gaban wasu gine-gine da ya lalace domin zaƙulo waɗanda suka tsira da rai.

Comments

Popular posts from this blog

Yanzu-Yanzu: Babbar kotun koli Ta Kasa Nigeria Ta Umarci Jam'iyyar PDP Ta Bai wa Tsohon Gwamnan Jigawa Daman Fitowa Takarar Shugabanci Jam'iyyar.

Abun-Mamaki: Wajen Jana'izar Sheik Dahiru Usman Bauchi /Sababbin kabarai na hausa EagleNewsHausa

Ana Wata Ga Wata: 'Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Mata 12.