Yanzu-Ynazu: Israela Ta Kashe Fasdinawa Goma(10)
Ma'aikatar Lafiyar Hamas Tace Isra'ila Ta Kashe Falasɗinawa 10.
Ma'aikatar lafiya a Falasɗinu ta ce hari ta sama da Isra'ila ta kai yamma da gaɓar kogin Jordan da ta mamaye ya hallaka aƙalla Falasɗinawa 10.
An kai harin ne a yankunan Tunbas da Samaria da ke arewacin kogin Jordan.
Wakilin BBC ya ce ƴan makonnin nan Isra'ila ta zafafa kai hare-haren soji a arewacin yamma da gaɓar Kogin Jordan musamman a Jenin, inda hukumomin Falasɗinu suka gwabza faɗa da Hamas da mayaƙan jihadi.
Hotunan bidiyo da ake kyautata zaton a garin Tamoun ne, ya nuna yadda mutane suka cika maƙil gaban wasu gine-gine da ya lalace domin zaƙulo waɗanda suka tsira da rai.

Comments
Post a Comment