Yanzu_Yanzu: An Kashe Mutane Sama Da 150 A Gaza

Akalla Mutane 150 Ne Suka Mutu A Cikin Kwanaki Biyu Da Isra'ila Ta Kai mummunan Hare-Hare Ta Sama A Zirin Gaza, Ciki Har Da Akalla Mutane 73 Da Aka Bayar Da Rahoton An Kashe Su A Ranar  Juma’a, Yayin Da 77 Aka Tabbatar An Kashe Su A Ranar Alhamis.

 Kungiyar kare hakkin bil adama ta ce tsare shugaban Asibitin Kamal Adwan Dr Hussam Abu Safia alama ce ta "nufin kisan kiyashi" a kokarin da Isra'ila ke yi na "kashe" bangaren kiwon lafiya na Gaza.

 Yayin da ake ci gaba da tattaunawa a Qatar, babban jami'in Hamas Basem Naim, ya ce kungiyar Falasdinawa da gaske take a kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da janyewar sojojin Isra'ila daga Gaza, da kuma mayar da al'ummar yankin zuwa gidajensu. 

Babban jami'in kare hakkin bil'adama na Majalisar Dinkin Duniya Volker Turk ya ce kungiyar ta duniya ta yi rikodin hare-hare 136 na Isra'ila a kan cibiyoyin kiwon lafiya 27 a Gaza, wanda ya haifar da "mummunan mutuwa , A Yakin Isra'ila a Gaza ya kashe akalla Falasdinawa 45,658 tare da raunata 108,583 tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.

 Akalla mutane 1,139 ne aka kashe a Isra'ila yayin hare-haren da Hamas ke jagoranta a wannan rana kuma sama da 200 aka kama.

Comments

Popular posts from this blog

Yanzu-Yanzu: Babbar kotun koli Ta Kasa Nigeria Ta Umarci Jam'iyyar PDP Ta Bai wa Tsohon Gwamnan Jigawa Daman Fitowa Takarar Shugabanci Jam'iyyar.

Abun-Mamaki: Wajen Jana'izar Sheik Dahiru Usman Bauchi /Sababbin kabarai na hausa EagleNewsHausa

Ana Wata Ga Wata: 'Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Mata 12.