Innalillahi! Ana Yin kurin Kai Hari Mummunan Ga Musulman Kudancin Nigeria.
Ana Yunkurin Farmakar Musulmai A Kudancin Najeriya,' Kungiyar MURIC Ta Tona Asiri.
Kungiyar MURIC ta zargi wasu kungiyoyi da shirin haddasa rikici kan batun kafa shari'ar Musulunci a Kudu maso Yamma.
A cewar MURIC, ana amfani da kafofin sada zumunta wajen tunzura jama’a da kuma yin barazana ga shugabannin Musulmi Kungiyar ta bukaci Shugaba Bola Tinubu ya tsawatarwa mutanensa da ke barazanar farmakar Musulamn da ke a Kudu.
Abuja - Kungiyar kare hakkin Musulmai (MURIC) ta zargi wasu kungiyoyi da shirin haddasa tashin hankali ga Musulmin Kudu maso Yamma.
Kungiyar ta bukaci Sufeto Janar na ‘yan sanda, Darakta Janar na DSS da sauran jami’an tsaro su dakile yunkurin kuma su kare rayukan Musulmi.
MURIC na zargin ana shirin farmakar Musulmai MURIC ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da daraktan kungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya fitar a ranar Juma’a kamar yadda The Guardian ta ruwaito.

Comments
Post a Comment