Yanzu-Ynazu: Israela Ta Gar Gadi Hamas Da Ta Saki Israelawan Da TA Kama
Isra'ila Tace Dole Hamas Ta Saki Isra'ilawa Uku Masu Rai A Ranar Asabar.
Isra'ila ta ce dole ne Hamas ta saki aƙalla Isra'ilawa uku masu rai a ranar Asabar idan har ana so a ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wutar.
Mai magana da yawun ƙasar, David Mercer ne ya bayyana hakan, bayan Hamas ta sanar da sakin Isra'ilawa uku a ranar Asabar ɗin.
Tun da farko ƙungiyar ta ce za ta dakatar da sakin Isra'ilawan, bayan da ta zargi Isra'ila da karya sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wutar, saboda hana shigar da kayan buƙatu zuwa Gaza.

Comments
Post a Comment