Posts

Da Dumi-Dumi: Tsohon Gwamnan Kogi Yahayya Bello Zai Gabatar Da kansa A Gaban Kotun.

Image
  Tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello Zai Gabatar Da Kansa A Gaban Kotu Ranar 13 Ga Watan Yuni Tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello Zai Gabatar Da Kansa A Gaban Kotu Ranar 13 Ga Watan Yuni Bayan kai ruwa rana, daga karshe dai tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya amince ya mika kansa a gaban kotun tarayya da ke Abuja a ranar 13 ga watan Yuni kan tuhume-tuhumen da hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) take yi masa kan almundahanar makudan kudade. Lauyan da ke tsayawa, Yahaya Bello, Abdulwahab Mohammed, ya yi wa mai shari’a Emeka Nwite, alkawari a ranar Juma’a, bayan kotun ta ki amincewa da bukatar dakatar da shari’ar da wanda ake kara ke yi. Zargin Badakala: Tataburzar EFCC Da Yahaya Bello Na Daukar Sabon Salo, Zan Yi Murabus Matukar Ba A Gurfanar Da Yahaya Bello Ba Shugaban EFCC. Muhammad ya ce tsohon gwamnan baya tsoron a gurfanar a gaban kotu ko kadan. Lauyan tsohon gwamnan ya shaida wa kotun cewa, rayuwar wanda yake karewa na fuskantar barazana a Abuja, ...

Da Dumi-Dumi: Tsare "Daniel Ojukwu" Barazana Ne Ga 'Yancin Aikin Jarida A Nigeria

Image
Tsare Daniel Ojukwu Barazana Ne Ga Ƴancin Aikin Jarida A Najeriya  HRW Ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Human Rights Watch ta ce tsare ɗan jaridar nan a Najeriya, Daniel Ojukwu ya take ƴancinsa a matsayin mai bayar da rahoto. Ƙungiyar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar wadda ta aike wa kafafen yaɗa labarai a Najeriya. HRW ta nemi hukumomin Najeriya su gaggauta sakin Ojukwu idan ba a tuhume shi da aikata babban laifi ba. A cewar ƙungiyar, ƴan jarida da ƙungiyoyin kare haƙƙin bil adama a Najeriya na zanga-zanga kan kama Daniel Ojukwu tare da tsare shi. Ɗan jaridar da ke aiki a gidauniyar aikin jarida na bin diddigi, ya ɓata ne a ranar 1 ga watan Mayu. Daga bisani kuma an gano cewa yana hannun ƴan sanda, inda aka zarge shi da take dokar yaƙi da laifukan intanet ta Najeriya. Ƙungiyar ta ƙara da cewa hukumomi sun yi ta watangaririya da shi a tsakanin ofisoshin ƴan sanda har da cibiyar daƙile laifukan intanet da sashen binciken manyan laifuka a Abuja. HWR ya ce kundin tsarin ...

Da Dumi-Dumi: Biden Yafadi Dalilin Da yasa Bai Bawa Isra'ila Bama-Bamai Ba Don Yaƙin Rafah

Image
Dalilin Da Ya Sa Biden Ya Ƙi Bai Wa Isra'ila Manyan Bamabamai Don Yaƙi A Rafah. Yanzu haka dai an kwashe kimanin watanni bakwai kenan Isra'ila na yaƙi a Gaza kuma ana ci gaba da samun rasa rayuka. To sai dai a yanzu kuma shugaban ƙasar Amurka, Joe Biden a wata tattaunawa da gidan talbijin na CNN, ya yi bayani kan dalilin da ya sa ya dakatar da aikewa da wasu manyan makamai mafi ƙarfi da Amurka ke da su zuwa Isra'ila. Makaman sun haɗa da bamabamai masu ƙarfi nau'in 2000lb. Abin tambaya shi ne mene ne illar da bamabaman za su yi idan aka jefo su daga sama? A matsayinsa na makamin yaƙi, bam ɗin nau'in 2000lb yana da mummunar illar da zai haddasa. Majalisar Dinkin Duniya ta ce bam ɗin yana da ɓuraguzan da ke kisa daga nisan mita 350, sannan ɓaraguzan za su iya fasa ginin kankare mai kaurin mita uku sannan ya samar da rami mai girman mita 15. Hakan ne ya sa ake ganin rashin dacewar yin amfani da shi a wurin da ke da dandazon farar hula kamar birnin Rafah. Ko da mutanen d...

Yanzu-Yanzu: Kotu Ta Bada Belin Hadi Sirika Tare Da 'Yar Sa

Image
  Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bayar da belin tsohon ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da ‘yarsa, Fatima bayan sun gurfana a gabanta a yau. An bayar da belinsu ne kan kudi Naira miliyan 100 kowannensu. Mun Kawo Jam’iyyar AAC Ne Domin Al’ummar Adamawa – Doubli.   Nijeriya Ta Musanta Iƙirarin Binance Na Zargin Cin Hancin Dala Miliyan 150. Har wa yau, kotun ta bayar da belin wasu mutane biyu da aka gurfanar da su tare kan kudi Naira miliyan 100. Ana zargin Sirika ne da sauran mutanen da laifin almundahanar kudi Naira biliyan 2.7 a lokacin da yake rike da mukamin minista.   Sauran ka’idojin belin sun hada da kawo wadanda za su tsaya musu wadanda suka mallaki kadarori a Abuja. Labarai Masu Nasaba CBN Ya Bayyana Sunayen Bankuna 41 Da Ya Aminta Da Ingancinsu A Nijeriya  Rashin Tsaro: Majalisa Ta Nemi Sojoji Su Ƙaddamar Da Shiri Na Musamman Don Kakkaɓe Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Neja. Idan ba a manta ba h...

Da Dumi-Dumi: 'Yan Wasan Bayer Munich Sunce,"Dakatar Da Wasan Da Rafali Yayi yaudarane".

Image
Dakatar Da Wasa Da Lafari Ya Yi Kafin Mu Farke Ƙwallo Yaudara Ce Kawai. Kocin Bayern Munich Thomas Tuchel ya ce dakatar da wasa da alƙalin wasa ya yi kafin tawagarsa ta farke ƙwallon da Real Madrid ta zira musu "kamar yaudara ce". Bayern ce ke kan gaba da 0-1 bayan dawowa daga hutun rabin lokaci a wasan gab da ƙarshe na Champions League har zuwa minti na 88, lokacin da Joselu ya ci biyu cikin minti uku. Bayan haka ne kuma a minti na 13 bayan cikar lokaci, Matthijs de Ligt ya farke ƙwallon amma kuma mataimakin lafari ya ɗaga tutar satar-gida. 'Yan wasan Real Madrid sun tsaya da wasan kafin De Light ya zira ƙwallon a raga, amma sai daga baya aka ga akwai yiwuwar babu satar-gidan kuma da na'urar VAR ta duba hukuncin.  Saboda an tsayar da wasan, VAR ba za ta iya yin komai ba.  Tuchel ya faɗa wa TNT Sports cewa "hukunci ne mummunan gaske" wanda kuma "ya saɓa wa dokoki". "Ana samu mummunan hukunci daga mataimakin lafari da kuma lafarin. Abin dai kam...

Yanzu -Yanzu: Gwamna Nasir Yabada Tallafin Sama Da Naira Milyan 80 Ga Kungiyar Lauyoyin Kebbi.

Image
Gwamna Nasir Ya Bada Gudunmuwar Naira Miliyan 100 Ga Kungiyar Lauyoyi Kan Gina Sakatariya A Kebbi. Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 100 ga kungiyar lauyoyi ta Nijeriya (NBA), domin gina sakatariyarta reshen jihar a Binrin Kebbi. Ya bayar da wannan gudummawar ne a lokacin kaddamar da kwamitin gyaran fuska na shari’a, kwamitin gudanarwa da kuma kaddamar da wasu karin sassa biyu a ma’aikatar shari’a ta jihar. Sojojin Nijar Sun Kama Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Nijeriya, Kachallah Mai Daji Hauhawar Farashin Siminti: Majalisa Ta Bai Wa Dangote, BUA, Da Sauransu Wa’adin Kwanaki 14 Su Bayyana Gabanta. Ya kuma ba da tabbacin cewa, gwamnatinsa za ta samar wa alkalai da lauyoyi hanyoyin sufurin da suka dace, yana mai cewa ya samar da kudaden da za a gyara ababen hawansu. “Ina girmama bangaren shari’a, kuma na kuduri aniyar kawo sauyi a bangaren domin a gaggauta gudanar da ayyukan adalci da kuma samun adalci ga kowa, ba tare da tsangwama ba. Gwam...

Wata Sabuwa: Majalisar Wakilai Ta Muasanta Zargin Tayin Cin Hancin Binance.

Image
  Majalisar Wakilai Ta Musanta Zargin Tayin Cin Hancin Binance, Zata Binciki Arcewar Anjarwalla Daga Hannun Jami’an Tsaro. Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar ta yanke shawarar gudanar da bincike akan yadda wani babban jami’in kamfanin Binance, Nadeem Anjarwalla, ya arce daga hannun jami’an tsaron Ofishin Mashawarcin Shugaban Kasa Akan Harkokin Tsaro a watan Maris din daya gabata. Majalisar Wakilan Najeriya ta musanta batun neman cin hanci daga rukunin kamfanonin Binance, sakamakon zargin baya-bayan nan da kamfanin hada-hadar kudin kirfto din yayi. A jiya Talata ne binace ya bayyana cewar wasu mutane daga Najeriya da ba’a san ko su wanene ba, sun bukaci ya biyasu makudan kudaden intanet “domin taimakawa wajen warware matsalolin kamfanin a kasar”. Kamfanin ya kara da cewar an tunkari wakilansa bayan da suka bar wurin ganawar da suka yi da kwamitin Majalisar Wakilai akan laifuffukan da suka shafi kudi. Binance KU DUBA WANNAN MA ‘Yan Sandan Kenya Sun Kama Wani Shugaban Bina...