Posts

Showing posts from March, 2024

Louis Gossett Jr., 'Jami'i kuma Mutumin Karramawa' Oscar Champ, Ya Ciji Kura Yana Da Shekara 87.

Image
  Louis Gossett Jr., 'Jami'i kuma Mutumin Karramawa' Oscar Champ, Ya Ciji Kura Yana Da Shekara 87.  Wanda ya lashe kyautar Oscar mai goyon bayan wasan kwaikwayo don wasa malamin wasan motsa jiki a cikin 1982 "Jami'i kuma Mutum ne Mai girma" shekaru biyu bayan nasarar lashe Emmy don aikinsa a matsayin fiddler mai fasaha a "Roots," ya mutu a safiyar Juma'a. safe. Ya kasance 87.  Iyalin Gossett sun ba da sanarwar rasuwarsa a cikin wata shela, suna mai cewa: "Ya kasance tare da kukanmu na gaske don tabbatar da cewa mahaifinmu mai ƙauna ya mutu a yau. Muna iya gode wa kowa da kowa don juyayinsu a yanzu. Idan ba matsala bace, kula da kariya ta iyali. a wannan lokaci mai wahala."  A cikin Taylor Hackford's "Jami'i kuma Mutum Mai Girma," Gossett's Sgt. Emil Foley musamman ya kori halayen Richard Gere zuwa alamar kusa da shiga makarantar jirgin sojojin ruwa. Gossett shine babban mutum mai launi don lashe Oscar Mafi Tal...

QASAR SAUDI ARABIA ZATA SHIGA GASAR KYAU NA DUNIYA

Image
Karo  Na Farko A Tarihi, Rumy Alqahtani, 'Yar Kasar Saudiyya, Za Ta Yi Gasar Kyawun Miss Universe 2024. Wannan dai wani gagarumin sauyi ne a sauye-sauyen da yariman masarautar Saudiyya Mohammed Bin Salman ke jagoranta. Alqahtani mai shekaru 27 da haihuwa, haifaffen birnin Riyadh, ya yi amfani da shafin sada zumunta na Instagram wajen jaddada muhimmancin fara gasar tarihi da al'ummar kasar ke da shi a gasar kawata baya ga nuna farin cikinta da samun damar. Da wannan sanarwar, Alqahtani ya zama dan takara na biyu daga yankin Gulf masu ra'ayin mazan jiya don fafatawa a gasar Miss Universe, bayan Lujane Yacoub na Baharain, wanda ya halarci shekarar da ta gabata. Iran za ta shiga gasar Miss Universe a karon farko a ranar 18 ga watan Satumba, wanda za a yi a Mexico. Alqahtani, Tani likitan hakori ne wanda ya yi digirinsa na farko a cikin yaruka uku: Larabci, Faransanci, da Ingilishi, a cewar The Independent. An ba ta sarautar 2021 Miss Arab World Peace, Miss Saudi Arabi...

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Abin Da Ya Kira “Ayyukan Da Ba Su Dace Ba” Da Masu Garkuwa Da Mutane Ke Aikatawa A Fadin Kasar Nan

Image
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Abin Da Ya Kira “Ayyukan Da Ba Su Dace Ba” Da Masu Garkuwa Da Mutane Ke Aikatawa A Fadin Kasar Nan, Yana Mai Cewa Wadanda Ke Da Hannu A Irin Wadannan Munanan Laifuka Dole Ne A Kawo Karshen Su. Shugaban ya bayyana haka ne a jiya ranar Talata a liyafar cin abinci na watan Ramadan tare da mambobin ma’aikatan shari’a na tarayya karkashin jagorancin Alkalin Alkalan Najeriya (CJN),  Tinubu, wanda ya sake sabunta kudirin gwamnati na fatattakar ‘yan fashi, ya ce wadanda suka koma sace yara matsorata ne, wadanda ba za su iya tinkarar karfin sojojin Najeriya ba.

Gwamna Zulum Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Aka Jima Ba A Ji Ƴan Ta'adda Sun Sace Dalibai Daga Makarantu A Jihar Barno

Image
Gwamna Zulum Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Aka Jima Ba A Ji Ƴan Ta'adda Sun Sace Dalibai Daga Makarantu A Jihar Barno . Farfesa Babagana Zulum ya ce shirin samar da aminci a makarantu da suka kaddamar shekaru 7 zuwa 8 da suka wuce ya yi aiki yadda ya kamata Ya ce shirin ya gina katanga a mafi yawan makarantu kuma jami'an hukumomin tsaro na aiki tare domin tabbatar da tsaro  Zulum ya ce baya ga yadda sojoji da sauran jami’an tsaro ke iya bakin ƙoƙarinsu, domin ganin cewa sun kawo karshen ta'addacin dake faruwa acikin jihar Borno. Yaqara da cewa jihar Barno tana amfani da mafarauta,da dama kamar:‘yan banga da kuma jami'an JTF da sauransu. domin yin qoqarin kare dukkan rayuka da dukiyoyin al'ummar da yake jagoranta.

A Jamhuriyar Nijar An Fara Samun Rarrabuwar Kawuna Tsakanin Kungiyoyin Farar Hula Masu Goyon Bayan Sojojin Da Ke Mulkin Kasar

Image
  A Jamhuriyar Nijar An Fara Samun Rarrabuwar Kawuna Tsakanin Kungiyoyin Farar Hula Masu Goyon Bayan Sojojin Da Ke Mulkin Kasar, Yayin Da Wasu Ke Goyon Bayan Kasashe Irin Su Rasha, Wasu Na Cewa Nijar Ba Ta Bukatar Sojojin Wata Kasa Ta Waje. Kungiyar da ke kare fararen hula ta MNSP ta ce muddin bayanai suka tabbatar da cewa akwai sa-hannun wata kasa a kisan da aka yi wa sojojin Nijar din 23 tare da jikkata 17, shakka babu za ta gabatar da korafin gaban Majalisar Dinkin Duniya. Amma kungiyar ta ce akwai bukatar gwamnatin sojin kasar ta karfafa alakar da ke tsakaninta da kasashe irin su Rasha da sauransu. Kodayake kungiyoyi irin su M62 na ganin cewa babu bukatar dauko dakarun wata kasa domin aikin wanzar da zaman lafiya a Nijar, yayin da suke zargin wanzuwar irin wadannan dakarun shi ke rura wutar rikicin da ke faruwa a kasar.

Gwamnan Jihar Zamfara A Arewacin Najeeriya, Dauda Lawal, Ya Ce Ya Gabatar Wa Shugabannin Tsaron Ƙasa Sabbin Buƙatu Da Zimmar Daƙile Hare-haren 'Yan Fashin Daji A Jihar Tasa.

Image
Gwamnan Jihar Zamfara  Arewacin Najeeriya, Dauda Lawal, Ya Ce Ya Gabatar Wa Shugabannin Tsaron Ƙasa Sabbin Buƙatu Da Zimmar Daƙile Hare-haren 'Yan  Fashin Daji A Jihar Tasa. A ranar Talata ne gwamnan ya je birnin Abuja, inda ya gana da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, da Nuhu Ribadu mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro. Haka nan, gwwamnan ya faɗa cewa bincikensu ya gano cewa ana kwashe wasu daga cikin sojojin da ke Zamfara tare da sauya musu wurin aiki, inda ya ce ya nemi a ƙara yawansu a jihar.

Hedkwatar Tsaron Amurka Ta Shaida Wa 'Ƴan Majalisar Dokokin Ƙasar Ranar Alhamis Cewa A HukumanceBa Su Bai Wa Dakarun Amurka Umarnin Barin Ƙasar Ba

Image
  Hedkwatar Tsaron Amurka Ta Shaida Wa 'Ƴan Majalisar Dokokin Ƙasar Ranar Alhamis Cewa A Hukumance Sojojin Nijar Ba Su Bai Wa Dakarun Amurka Umarnin Barin Ƙasar Ba, Tana Mai Cewa Ta Samu Bayanai Masu Harshen-Damo Kan Matakin Korar Dakarun Nasu Daga Nijar. Celeste Wallander, mataimakiyar sakataren tsaron Amurka kan ƙasashen duniya, ta shaida wa Kwamitin Harkokin Sojoji na Majalisar Wakilan ƙasar cewa a hukumance kawo yanzu gwamnatin sojojin Nijar, wadda aka fi sani da CNSP, ba ta umarci sojojin Amurka su fita daga ƙasar ba. Wallander ta ce gwamnatin sojin Nijar ta soke yarjejeniyar da ta bai wa dakarun Amurka damar zama a ƙasar. Amma ta ce sojojin sun "tabbatar mana cewa za a kare lafiyar dakarun Amurka kuma ba za su ɗauki wani mataki da zai cutar da su ba.” Amurka tana da dakaru kusan 650 tare da ɗaruruwan masu taimaka musu a Nijar, inda suke yaƙi da ta'addanci. Sai dai a watan Yulin da ya gabata sojoji sun kifar da gwamnatin dimokuraɗiyya sannan daga bisani suka kori daka...

An Gurfanar Da Fitacciyar Jarumar Fina-finan Hausa, Amal Umar

Image
  An Gurfanar Da Fitacciyar Jarumar Fina-finan Hausa Ta Kannywood Gaban Kotun Majistre Da Ke Gyaɗi-Gyaɗi A Birnin Kano Bisa Zargin Yunƙurin Bai Wa Ɗansanda Cin Hanci. Ana zargin Amal da yunƙurin ba da cin hancin naira dubu 250 ga wani ɗan sanda mai suna ASP Salisu Bujama da ke rundunar ƴansandan, shiyya ta ɗaya da ke Kano. A cewar mai gabatar da ƙarar, Amal na yunƙurin bayar da cin hancin ne domin hana binciken ƴan sanda kan zargin saurayinta da almundahanar kuɗi. Lamarin ya bayyana ne lokacin da wani Yusuf Adamu ta hannun lauyansa ya shigar da ƙorafi ga mataimakin babban spetan ƴansanda Umar Mohammad Sanda, inda yake zargin saurayin jarumar da yin sama da faɗi da kuɗin da ya kai naira miliyan 40 da sunan kasuwanci. Ƙorafin da aka shigar ya sa ƴansanda gudanar da bincike wanda ya gano cewa saurayin jarumar ya tura mata naira miliyan 13 ta asusun bankinta. Acewar kakakin rundunar ƴansanda shiyya ta ɗaya, CSP Bashir Muhammed, an gayyaci ƴar fim ɗin domin amsa tambayoyi daga bisani ku...

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Ƙarin Albashi Da Alawus-alawus Ga Alƙalai

Image
A Ranar Laraba Ne Majalisar Wakilai Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Neman Ƙarin Albashi Da Alawus-alawus Ga Alƙalan Najeriya. Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu ya miƙa wa Majalisar kudirin dokar domin tantancewa tare da amincewa da shi a ranar Talata. Ƙudirin da aka amince da shi ya bayar da albashin jimlar naira miliyan 5.3 a kowane wata ga alƙalin alƙalai na Najeriya (CJN). Ƙudirin ya kuma ce sauran alkalan Kotun Koli za su samu albashin naira 4.2 yayin da Shugaban Kotun ɗaukaka ƙara zai rika samun albashin naira miliyan 4.4 duk wata. Haka kuma, alƙalan kotun ɗaukaka ƙara za su rika karɓar albashin naira miliyan 3.7 duk wata, yayin da ƙaramin alƙali zai karɓi albashin naira miliyan 3.5 duk wata. A cewar ƙudirin, albashin na wata-wata ya kunshi cikakken albashinsu ne da duk wani alawus-alawus na yau da kullum da suka haɗa da samar da mai da kuma kula da ababen hawa da dai sauransu.