Posts

Showing posts from May, 2024

Yanzu-Yanzu: "Yadda Za A Magance Rashin Tsaro A Nigeria," Daga Bakin Kodinaitan Arewa

Image
Hanya Mafi Sauki Da Za A Magance Matsalar Tsaro A Katsina Gamayyar Kungiyoyin Arewa. Babban kodinaita na gamayyar kungiyoyin arewa na Jihar Katsina, Habibu Ruma ya bayyana wasu hanyoyi da suke ganin idan gwamnatin Jihar Katsina ta yi amfani da su za a iya samun nasara kan matsalar tsaron da ta addibi jihar da yankin arewa baki daya. Kodinaitan gamayyar kungiyoyin ya yi wannan karin haske ne a lokacin da suka shirya wani taro domin fadakar da ‘ya‘yan kungiyar halin da yanayin da tsaro ya samu kanshi a Jihar Katsina da kuma arewa baki daya. Matsayar Ƙungiyar Sarakunan Arewa A Tsaya Kan Umarnin Kotu Kan Rikicin Sarki 2 A Kan. Mun Dukafa Kawo Karshen Matsalar Wuta A Arewa Maso Gabas – Gwamna Inuwa .Habibu wanda ya yi bitar cewa matsalar tsaro a Jihar Katsina da kuma arewacin Nijeriya ta kassara duk wani ci gaba a bangaren ilimi da haifar da jahilci da rashin shugabanci da shan miyagun kwayoyi wanda har gobe sune ake gani matsayin dalilin faruwar haka. Yana mai cewa farmakin da ‘yan bindiga...

Da Dumi-Dumi: An Maka Gwamnoni Kotun Koli Abisa Wasu Dalilai

Image
Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi: Gwamnoni Sun Shiga Dimuwa Bisa Maka Su A Kotun Koli Sakatariyar kungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF) ta ki cewa uffan kan batun da gwamnatin tarayya ta kai karar gwamnonin jihohin tarayya 36 a gaban kotun koli bisa zargin rashin sakar wa kananan hukumomi mara. Lokacin da aka tuntubi, Babban Daraktan NGF, Dakta Abdulateef Shittu ya bayyana cewa sakatariyar ta karanta rahoton, ya ce tun da dai batun ya riga ya shiga kotu, musamman kotun koli, zai iya magana a kai ba. Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba. Rikicin Masarautar Kano: Lauyoyi Da Alƙalai Sun Tozarta Ɓangaren Shari’a – Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi. Ya ce, “Sakatariyar NGF tana sane da cewa gwamnatin tarayya ta dauki matakin shari’a kan gwamnonin jihohi 36 na tarayya a gaban kotun koli bisa zargin rashin sakar wa kananan hukumomin mara ta yadda za su dunga cin gashin kansu. Tun da al’amarin yana gaban kotu, ba za a iya cewa komin ba har sai kotun koli ta zartar da hukuncinta. ” Idan d...

Yanzu-Yanzu: Sojoji Sun Kashe 'Yan Bindiga Sama Da 624; Da Nasarar kama 1,051

Image
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 624, Sun Kama 1,051 A Watan Mayu – DHQ Dakarun rundunar sojin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda 624, sun kuma kama 1,051 ciki har da masu kai musu rahoto, sannan sun ceto mutane 563 a watan Mayu, 2024. Daraktan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Edward Buba ne, ya bayyana hakan ga ‘yan jarida a Abuja. ‘Yancin Kananan Hukumomi: Kotun Koli Ta Bai Wa Jihohi 36 Kwana 7 Su Kare Kansu Ina Kokarin Cika Alkawuran Da Na Dauka – Tinubu. Ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya da su kasance masu goyon bayan sojoji wajen yaki da ta’addanci da ‘yan fashi da sauran laifuka daban-daban. Buba ya sake nanata cewa al’ummar kasar nan na da irin rawar da za su taka wajen kawo karshen hare-haren ta’addancin a fadin kasar nan. Kakakin tsaron ya kuma bayyana cewar dakarun sun kwato makamai guda 707. Labarai Masu Nasaba Ina Kokarin Cika Alkawuran Da Na Dauka – Tinubu  Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara Ya ce sun kuma gano bindigogi kirar AK-47 guda 41...

Yanzu-Yanzu: An Kama Babban Dan Bindigan Da Ya Addabi Zamfara

Image
  Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara Jami’an tsaro a Jamhuriyar Nijar sun cafke daya daga cikin kasurguman ‘yan bindigar da suka addabin jama’a musamman a cikin Jihar Zamfara wanda aka fi sani da suna Baleri.  A ranar Talata ne runduna ta musamman da ake kira ‘’Farautar Bushiya” ta cafke Balari da wasu dimbin yaransa a garin Tankama da ke yankin Gidan Runji a Jihar Maradi daf da iyakar Nijeriya da Nijar. An Kashe Masunta 31, 40 Sun Yi Ɓatan Dabo A Wani Harin ‘Yan Ta’adda A Borno. An Kashe Mutane 5000, An Sace 7000 Cikin Shekara 1 A Mulkin Tinubu – Bincike. Jami’an tsaron sun kai samame ne a Rugar Kowa Gwani bayan da suka samu bayanan sirri da ke cewa ‘yan bindigar dauke da makamai sun tattaru a wannan kauye. Lokacin da yake gabatar da ‘yan bindigar a gaban mahukunta, babban kwamandan rundunar ta ‘’Farautar Bushiya’’ Kanar Mohamed Almoctar Niandou, ya ce za su ci gaba da jajircewa domin tabbatar da tsaro a kan iyakokin kasashen biyu. Baleri, ya...

Da Dumi-Dumi: An Kori Ɗaliban Najeriya A Kasar Burtaniya.

Image
Yadda Faduwar Darajar Naira Ta Sa Aka Kori Ɗaliban Najeriya Daga Birtaniya. An kori wasu ɗalibai ƴan Najeriya daga makaranta tare da ba su umarnin barin Birtaniya saboda gazawa wajen biyan kuɗin makaranta sakamakon faɗuwar darajar kuɗin ƙasar tasu naira. Hakan dai ya faru ne a Jami'ar Teesside, wadda ta dakatar da ɗaliban daga shiga aji saboda rashin biyan kuɗin makaranta a kan lokaci. Wasu daga cikin waɗanda lamarin ya shafa sun shaida wa BBC cewa, matakin Jami'ar ya sanya sun ji kamar su kashe kansu, inda suka zargi jami'ar da ɗaukar mataki na rashin tausayi. Mai magana da yawun Jami'ar ya ce rashin biyan kuɗin makaranta ya saɓawa dokar izinin zaman ƙasar, lamarin da ya sa suka sanar da hukumar shigi da fici ta ƙasar halin da ɗaliban suke ciki. Najeriya dai na fama da matsin tattalin arziƙi da faɗuwar darajar kuɗin ƙasar naira, lamarin da ya jefa da yawan ɗaliban ƙasar da ke karatu a Birtaniya cikin halin ha'ula'i. Tashin farashin kayayyaki ya ƙaru da kashi 30...

Puskas Arena Zai Karbi Ga Garumin Wasan Karshe A Champions League

Image
Puskas Arena Zai Karbi Wasan Karshe A Champions League 2026 Za a buga wasan karshe a Champions League a 2026 a Budapest a filin da ake kira Puskas Arena, inji Uefa ranar Laraba, bayan tashi daga babban taron da ta gudanar a Dublin. Filin dake cin ƴan kallo 67,215 shine wajen da tawagar Hungary ke buga wasanni, wanda ya karbi bakuncin wasa hudu a Euro 2020 da na karshe a Europa League tsakanin Sevilla da Roma. An ɗage taron zabar filin da zai shirya wasan karshe a 2027 zuwa watan Satumba, bayan da Uefa ke son jin karin bayani kan shirin gyaran San Siro, inda AC Milan da Inter ke wasanni. Haka kuma Uefa ta sanar da cewar za a buga wasan karshe a Champions League na mata a 2026 a Norway, Ullevaal Stadion. Shi kuwa filin wasa na Besiktas Park a Turkiya, zai shirya karawar karshe a Europa League a 2026 da kuma Europa Conference League a 2027. Jamus za ta karbi bakuncin wasa biyu - Filin wasa na Frankfurk zai shirya wasan karshe a Europa League a 2027 da kuma Europa Conference League a 2026 ...

Da Dumi-Dumi: 'Yan Sanda sun Yi Nasarar Ceto Mutanen Da A kayi Garkuwa Dasu A Abuja

Image
‘ Yan sanda Sun Ceto Wadanda Aka Yi Garkuwa Da Su A Abuja An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa Jami’an Rundunar ‘Yansanda ta birnin tarayya, Abuja, karkashin jagorancin kwamishina CP Benneth Igweh, sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a unguwar Dawaki da ke Abuja ranar Lahadi.  Kakakin rundunar ‘Yansandan birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce, cikin gaggawa da dabaru na mayar da martani ga harin da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai a garin Dawaki a ranar 19 ga Mayun shekarar 2024, da misalin karfe 11:30 na dare, jami’an rundunar karkashin jagorancin Kwamishinan CP Igweh, da kansa sun yi gaggawar zuwa inda lamarin ya faru. Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla? Mi’ara Koma Baya: CBN Ya Janye Dokar Cazar Kaso 0.05 A Banki Cikin jarumtaka da hadin kai, ‘yansanda tare da hadin gwiwa da mafarauta, suka ci g...

Da Dumi-Dumi: Haƙi Ƙanin Abun Da Ya Faru Agame Da Mutuwar Shugaban Kasar Iraƙ

Image
An Gano Gawar Shugaban Kasar Iran,  E brahim Raisi A Wajen Da Jirginsu Ya Yi Hatsari. Shugaban na Iran Ebrahim Raisi ya samu rakiyar Ministan Harkokin Ƙasashen Waje Amira dollarIan, da gwamnan yankin Azebaijan ta Gabas a Iran da sauran jami’ai da masu kare lafiyar shugaban ƙasa.  An gano gawar Shugaban Iran Ebrahim Raisi da ministan harkokin wajen ƙasar da sauran jami’ai a wajen da jirgi mai saukar ungulu ya yi hatsari, bayan an shafe sa’o’i ana nemansu a wani yanki mai tsaunuka da rashin kyawun hanya a arewa maso yammacin ƙasar, a cewar kafar watsa labaran gwamnati. Gidan talbijin na ƙasar bai bayar da bayanai kan dalilin hatsarin jirgin ba a yankin Azebaijan ta Gabas a Iran.  Sauran waɗanda suke cikin jirgin sun haɗa da Ayatollah Mohammad Ali Al-e Hashem - limamin masallacin Juma'a na birnin Tabriz da Janar Malek Rahmati watau gwamnan lardin gabashin Azebaijan.  Kwamandan askarawan kare lafiyar shugaban ƙasa, Sardar Seyed Mehdi Mousavi, da waɗansu jami'an tsaron na...

Da Dumi-Dumi: Shalƙwatan Tsaro Ta karyata Rahoton Sace Mutum 500

Image
Shalƙwatar Tsaro Ta Karyata Rahoton Sace Mutane 500 A Zamfara Shalƙwatar tsaro ta ƙasa (DHQ) ta yi watsi da rahotan da ke ikirarin an sace mutane 500 da aka yi a ƙaramar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara. Daraktan yaɗa labarai na rundunar Sojin Manjo Janar Edward Buba, ya bayyana hakan ne a yau Juma’a cikin wata sanarwa inda yake cewa a zahiri an sace mutane huɗu ne kawai, saɓanin alƙalumman da ake yaɗawa. Wani Sojan Amurka Ya Bankawa Kansa Wuta Don Nuna Goyon Bayansa Ga Falasdinawa. Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Hanyar Tafiyarsu Ta Kai Hari Ga Al’ummar Jihar Kaduna Janar Buba ya jaddada cewa dakarun Operation Hadarin Daji suna aiki ne a cikin wani yanayi mai cike da ƙalubale, inda ya zama dole su magance haƙiƙanin gaskiya da kuma bayanan ɓata gari, musamman daga shafukan sada zumunta. Ya ƙara da cewa, maganar mutane 500 da aka yi garkuwa da su, wani ƙarin gishiri ne, inda aka tabbatar da sace mutane huɗu kawai. Buba ya kuma ba da tabbacin cewa sojojin za su ci gaba da mai da han...

Da Dumi-Dumi: Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ya Kaddamar Da Yaƙin Neman Ilimi

Image
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Ya Kaddamar Da Gangami Yakin Neman Ilimi Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kaddamar da gangamin yakin neman bunkasa ilimi da koyon aikin hannu da kuma na daidaiton jinsi. Gangamin mai taken “Dukkaninmu Daya Muke” kungiyar matan shugabannin kasashen Afrika (OAFLAD) ce ta gabatar da tsarawa. Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano  An kaddamar da gangamin a kasashe 15 da ke da manufar bunkasa harkokin kiwon lafiya, ilimi, samar wa mutane ababen dogaro da kai na sana’o’i, da kuma yaki da cin zarafin jinsi. Nijeriya wacce ta dauki shirin wajen maida hankali kan taken cewa ilimi shi ne babban hanya na kawo canji, wanda matar shugaban kasa Sanata Senator Oluremi Tinubu ta gabatar. Da yake kaddamar da gangamin a fadar shugaban kasa, Tinubu ya jinjina wa kokarin matan shugabannin kasashen Afrika, da suka kasance masu maida hankali waje...

Yanzu-Yanzu: Barcelona Zata Kori Xavi Saboda Wasu Dalilai .

Image
Da Dumi-Dumi: Barcelona Daya Daga Cikin shahararrun ƙungiyar wasan kwallon Kafa Na Tunanin korar Xavi. Kungiyar Barcelona na duba yiwuwar korar kocin tawagarta Xavi. A cikin watan Junairu ne, dan shekaru 44 din ya bayyana cewa zai sauka daga mukaminsa a karshen kakar wasa ta bana, amma sai shugaban kungiyar Joan Laporta ya lallashe shi, sai ya sauya shawara. Amma kuma saboda kalamansa a tarukan manema labarai, a yanzu mahukunta kulob din suna fushi da shi kuma suna ganin ya kamata a raba gari da shi. Kocin tawagar karamar kungiyar Barcelona, Rafael Marquez ne ake tunanin zai maye gurbinsa. A ranar Alhamis bayan sun doke Almeria, Xavi ya ce akwai matukar wuya su iya gogayya da Real Madrid ta fannin kudi. "Ina tunanin ya kamata magoya bayan Barcelona su fahimta a kan yanayi mai sarkakiya da ake ciki, ba za su iya goga kafada da Real Madrid a Sifaniya ba da kuma sauran a nahiyar Turai," in ji Xavi. Real ta lashe gasar La Liga kuma a yanzu tana jiran buga wasan karshe a gasar zak...

Da Dumi-Dumi: 'Ibtila'in' Da Ya Faru Da Falasɗinawa A 1948

Image
Al-Nakba: 'Ibtila'in' Da Ya Faru Da Falasɗinawa A 1948 A kowace ranar 15 ga watan Mayu, Falasɗinawa a faɗin duniya na tunawa da ranar al-Nakba, wadda ke nufin 'bala'i'. Daga watannin ƙarshe na shekarar 1947 zuwa farko-farkon shekarar 1949, kimanin Falasɗinawa 750,000 suka zama ƴan gudun hijira, bayan tarwatsa su daga yankin da ya zama ƙasar Isra'ila.  Da dama daga cikin su an kore su ne da ƙarfi da yaji, yayin da wasu suka gudu domin tsira da ransa. Ranar Al-Nakba na tunawa ne da lokacin da aka kori Falasɗinawan daga gidajensu da kuma shekarun da suka kwashe suna gudun hijira. Lokaci na zaman ɗar-ɗar kuma an samu ɓarkewar rikice-rikice tsakanin Falasɗinawa da ƴan ƙasar Isra'ila a irin wannan rana a shekarun baya.  Ta yaya lamarin ya faru kuma me ya sa Falasɗinawa ke nuna "mabuɗin komawa"  a irin wannan rana? . Bayanan hoto,Falasɗinawa na ɗaukar makulli a matsayin wani tambarin ƴancinsu na komawa gidajensu da suka baro Yunƙurin kafa ƙasar Isra...

Hajjin Bana: Hukumar Aikin hajji Zata Taimaka Wa Alhazai.

Image
Hajjin Bana: Alamomin Da Za Su Taimaka Wa Alhazai Cikin Harsuna 16 Ciki Har Da Hausa. Hukumar Aikin Hajji da Umarah ta Kasar Saudiyya ta gabatar da wasu alamomi 15 da za su taimaka wa alhazai daga fadin duniya da za su gudanar da aikin hajjin bana a kasa mai tsarki. Wannan ci gaba na daga cikin tsare-tsaren da hukumar ta gabatar domin wayar da kan al’umma a yayin aikin hajjin bana na shekarar 1445 bayan hijira wanda ya yi daidai da 2024. Labarai masu nasaba: Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi Matashi Ya Banka Wa Masallaci Wuta Yayin Da Ake Sallah A Kano Hukumar ta sanar da hakan ne a shafukanta na kafofin sada zumunta da kuma shafinta na Intanet: https://guide.haj.gov.sa/ Hajjin Bana: Alamomin za su taimaka wa alhazai wajen yin tambayoyi cikin harsuna 16 da suka hada da Larabci, Inglishi, Faransanci, Urdu, Bengali, Indonesian, Hausa, Amharix, Persian, Spanish, Turkish, Russina, Sinhalese, Uzbek da yaren Malaysia. Labarai Masu Nasaba Hajjin Bana:...

Wata Sabuwa: An kama Wani Matashi Da Ya cinna Wa Masallaci Wuta

Image
‘ Yan Sanda Sun Kama Matashin Da Ya Cinna Wa Masallaci Wuta A Kano Rundunar ‘yansandan Jihar Kano, ta kama wani matashi da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta, yayin da mutane ke tsaka da sallar Asuba. Lamarin da ya faru a garin Larabar Abasawa da ke Karamar Hukumar Gezawa a Jihar, ya jikkata mutane da dama. An Dakatar Da Likita Saboda Sakaci A Jihar Kano Matashi Ya Banka Wa Masallaci Wuta Yayin Da Ake Sallah A Kano Cikin wata sanarwar da kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce matashin mai suna Shafi’u Abubakar mai shekaru 38 ya shiga hannunsu bayan wani bincike da suka gudanar. Hukumomin bayar da agaji a jihar sun mika akalla mutane 24 Asibitin Koyarwa na Murtala Muhammad da ke jihar, inda ake jinyar su. A gefe guda kuma wata majiya ta ce tuni mutum daya ya riga mu gidan gaskiya sakamakon munanan raunuka da ya samu sakamakon kunar wuta. Labarai Masu Nasaba Matashi Ya Banka Wa Masallaci Wuta Yayin Da Ake Sallah A Kano Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin ...

Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaron Zamfara

Image
‘ Yan Ta’adda 23 Sun Mutu A Rikicin ‘Yan Bindiga A Zamfara Bangarorin ‘yan bindiga biyu masu hamayya da juna daga tsagin Bello Kaura da Kachalla Najaja sun yi fito na fito da juna a kusa da dajin Sunke a karamar hukumar Anka a Jihar Zamfara. Eagle ta ruwaito cewa, bangarorin biyu sun shafe tsawon sa’o’i uku suna barin wuta a tsakaninsu, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar ‘yan ta’adda 23. Hukumar NSCDC Ta Kama Wasu Mutane 9 Da Ake Zargi Da Aikata Fashi A Kano Boko Haram Na Amfani Da Na’urar Starlink Ta Elon Musk Wajen Sadarwa Ta Yanar Gizo Kaura da Najaja, shugabannin ‘yan bindigar biyu sun yi arangama ne a dajin Sunke, inda suka yi musayar wuta. Tsagin Kaura sun yi nasarar fatattakar yaran Najaja, lamarin da ya tilasta musu tserewa cikin dajin Gandu da ke yankin Bukuyum a jihar. Wasu majiyoyi a yankin sun bayyana cewar fadan tsakanin tsagin biyu, ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu. Labarai Masu Nasaba Sojoji Sun Kashe Boko Haram 4 A Borno Gwamnatin Tarayya Ta Dak...

Yanzu-Yanzu: 'Yan Ta'adda Sun Sace Mutane Sama Da 75 A Wata Jaha

Image
' Yan ta'adda Sun Yi Nasarar Sace Mutane  sama da 'mutum 80' A Jihar Katsina. “ Sun ƙona gidana, sun ƙona ɗakunan matana da na iyayena, sun ƙona abincinmu, sun ƙona motata, akwai inji na huɗa wanda na siya 600,00 shi ma sun tafi da shi,” kamar yadda wani mazaunin ƙauyen 'Yar-Malamai ya shaida wa Eagle 🦅 Hausa. Katsina na daga cikin jihohin da ke fama da rashin tsaro a Nijeriya. ‘Yan ta’adda sun sace sama da mutum 80 a ƙauyen ‘Yar-Malamai da ke Ƙaramar Hukumar Faskari ta Jihar Katsina. Wannan na zuwa ne ƙasa da awa 24 bayan maharan sun kashe wasu sojoji a wani sansanin soji da ke yankin.  Mai magana da yawun ‘yan sandan Katsina ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya tabbatar wa TRT Afrika da faruwar lamarin, sai dai ya ce ba shi da cikakken bayani kan yadda harin ya kasance. Sai dai wani mazaunin yankin wanda ba ya so a ambaci sunansa ya shaida wa TRT Afrika Hausa cewa tun daga ranar Asabar ‘yan bindigan suka addabi yankin da hare-hare har zuwa ranar Litinin  . Ya bayyana c...

Yanzu-yanzu: Gwamnati Ta Dakatar Da Harajin Tsaron Intanet

Image
Yanzu-yanzu: Gwamnati Ta Dakatar Da Harajin Tsaron Intanet Kan Hada-hadar Kudade Gwamnatin tarayya ta dakatar da zabge kaso 0.5 cikin 10 na hada-hadar kudi da aka yi a yanar gizo domin biyan harajin tsaro na yanar gizo. Ministan yada labarai da wayar da kai, Mohammed Idris ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a ranar Talata bayan kammala taron kwanaki biyu na majalisar zartarwa ta tarayya da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a fadar shugaban kasa. Yanzu-yanzu: Gwamnati Ta Dakatar Cire Kaso 0.5 Na Tsaron Yanar Gizo Kan Hada-hadar Kudade Tsaron Yanar Gizo: TUC Ta Yi Barazanar Shiga Zanga-zanga A Nijeriya, A cewar sa, ana kan sake duba harajin amma yanzu dai, an dakatar da shirin. Idan ba a manta ba, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayar da umarni ga dukkan bankuna da cibiyoyin hada-hadar kudi, inda ya umarci a aiwatar da zabge harajin kaso 0.5 cikin 100 na tsaron yanar gizo kan duk wata hada-hadar kudi ta yanar gizo.  Sai dai, wannan umurni ya gamu da suka da turjiya ta bangare d...

Ana Wata Ga Wata: Mutanen Gaza Sama Da 440,000 Sun Gudu

Image
Gaza: Mutum 450,000 Sun Tsere Daga Rafah Cikin Mako Ɗaya - MDD Kimanin Falasɗinawa 450,000 ne suka tsere daga Rafah a cikin mako ɗaya da ya gabata, in ji Majalisar Ɗinkin Duniya, yayin da rahotanni ke cewa tankokin yaƙin Isra'ila na ci gaba da nausawa zuwa birnin da ke kudancin Gaza. Hukumar ayyuka da agaji ta MDD a yankin Falasɗinawa ta ce "al'umma na shan wahala kuma suna cikin yunwa da fargaba". Sojojin Isra'ila sun ce suna ci gaba da "kakkaɓe cibiyoyin ƴan ta'adda" a gabashin birnin, inda sama da mutane miliyan ɗaya ke samun mafaka. Sabbin hare-haren da Isara'ila ta ƙaddamar a arewacin Gaza sun tarwatsa wasu mutanen kimanin 100,000. Dakarun Isra'ila sun sake ƙaddamar da farmaki kan yankin Jabalia Zeitoun, inda sojojin Isra'ila suka ce mayaƙan Hamas sun sake yin sansani, wata biyar bayan Isra'ilar ta bayar da rahoton cewa ta kakkaɓe bataliyoyin Hamas a yankin. Sojojin Isra'ila sun buƙaci fararen hula su fice daga gabashin Rafah...

Da Dumi-Dumi: NMDPRA Ta Gana Da Dillalin Man Fetur

Image
NMDPRA Ta Gana Da Dillalan Man Fetur, Ta Sha Alwashin Biyan Bashin Naira Bilyan 200     A watan daya gabata, IPMAN tayi barazanar durkusar da harkar samarda man fetur a Najeriya, akan rashin biyan bashin Naira biliyan 200 ta kudaden dakon man. A yau Talata, Hukumar Kula da Cinikayyar Albarkatun Man Fetur a Najeriya (NMDPRA), ta gana da manyan dillalan man fetur da nufin magance matsalar yawan samun karancin man a kasar. Shugaban Hukumar ta NMDPRA, Farouk Ahmed, wanda ya shaidawa manema labarai yadda ganawar ta wakana, ya baiwa ‘yan Najeriya tabbacin cewar mamallaka rumbunar adana mai da mambobin Kungiyar Dillalan Man Fetur Mai Zaman Kanta (IPMAN) ba zasu dakatar da samarda man ba kasancewar NMDPRA ta fara shirye-shiryen biyan mamallaka rumbunan adana man basussukan da suke bi bayan tantance takardunsu. Injiniya Farouk Ahmed - NMDPRA Injiniya Farouk Ahmed - NMDPRA A watan daya gabata, IPMAN tayi barazanar durkusar da harkar samarda man fetur a Najeriya, akan rashin biyan bashin...

Da Dumi-Dumi: Kotun KOLI TA Daure Wani Mutum Wata Biyu A Gidan Yarin.

Image
Kotu Ta Daure Wani Mutum Wata 2 A Gidan Yari Kan Satar Doya Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu. Wata Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya, Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin daurin watanni biyu a gidan yari bisa samunsa da laifin satar doya da darajarta ya kai Naira 144,000. An yanke masa hukuncin ne kan laifin aikata laifuka da sata, amma ya roki kotun da ta yi masa sassauci. Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima’i A Benuwe. ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Sansanin Sojoji, Sun Kashe Dakaru 5 A Katsina. Alkalin kotun Jacinta Okeke, ta yanke wa Sani hukuncin zaman gidan yari na watanni biyu ko kuma yin aiki a kasuwar Gwagwalada. Ta kuma gargade shi da ya guji aikata laifuka. Tun da farko, lauya mai shigar da kara, Abdullahi Tanko, ya shaida wa kotun cewa mai shigar da kara, Liasu Saidu, na kauyen Ukara, ya kai rahoton lamarin ofishin ‘yansanda a ranar 9 ga watan Mayu. Labarai Masu Nasaba Buga Kudi: EFCC Za Ta Sake Gurfanar D...

Inalillahi! Wata Mata Ta Kashe Mijinta A Benewu

Image
Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima’i A Benuwe Wata matar aure mai shekaru 29 mai suna Torkwase Kpile ta daba wa mijinta wuka har lahira, bayan gardama ta barke a tsakaninsu saboda yawan jima’i a kauyen Achusa da ke karamar hukumar Makurdi a jihar Benuwe.  Eagle 🦅 Ta samu labarin cewa ma’auratan da suka yi aure watanni biyu da suka wuce, sun samu sabani kan yawan jima’i kafin matar ta dauki wuka ta daba wa mijin nata a wuya. ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 49 A Zamfara.  anata Hanga Ya Kare Sukar Da Ake Yi Masa Kan Tallafin Tukwanen Yumɓu Da Likafani An bayyana cewa ta daba wa mijin nata mai suna Igbah Kpile, wuka a sassa da dama na jikinsa wanda daga bisani rai ya yi halinsa. Ihun da mijin ya yi shi ya jawo hankalin makwabtansu, wadansa suka shiga gidan suka tarar da shi kwance cikin jini.  Tun da fari matar ta yi korafin cewar mijin nata yana yawan damunta da jima’i, wanda har ta kai da ta fara gajiya. Labarai Masu Nasaba An Yi Bikin Cikar Sarkin Lafiyan Bar...

Da Dumi-Dumi: Findi George Ya fara Aiki A Matsayin Sabon Mai horas Da 'Yan wasa

Image
  Finidi George Ya Fara Aiki A Matsayin Sabon Mai Horos Da ‘Yan Wasan Super Eagles Ta Nijeriya. Ministan wasanni, John Enoh, ya kaddamar da tsohon dan wasan Nijeriya, Finidi George, a   matsayin babban kociyan tawagar kwallon kafa ta Super Eagles a ranar Litinin a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja. Sabon Kociyan Kungiyar Kwallon Kafa ta Super Eagles, Finidi George, yayin da yake fara aiki a yau Litinin a Abuja. Sabon Kociyan Kungiyar Kwallon Kafa ta Super Eagles, Finidi George, yayin da yake fara aiki a yau Litinin a Abuja Sabon kocin na Super Eagles ya kuma zabi tsohon abokin wasansa na kasa, Daniel Amokachi da wasu ‘yan kasashen waje biyu a matsayin mataimakansa, Finidi ya bayyana hakan ne bayan bayyana shi ga manema labarai a hukumance a matsayin sabon koci a Abuja. NFF Za Ta Gabatar Da Finidi George A Matsayinl Sabon Kocin Super Eagles A Yau Litinin Kalubalen Da Ke Gaban Finidi George, Har ila yau ya kuma kuma bayyana Olatunji Baruwa a matsayin mai horar da mas...

Da Dumi-Dumi: Sarki Charles Na Burtaniya Ya Mika Mukaminsa Ga Ɗansa Bisa Wasu Dalilai

Image
Sarki Charles Na Birtaniya Ya Miƙa Muƙaminsa Na Babban Jami'in Soji Ga Ɗansa Yarima William Mai Jiran Gado A Wani Biki Da Aka Gudanar. "Babban abin shi ne ya kasance ya iya tuƙin jirgi," in ji Sarki Charles. Ba kasafai aka cika ganin Sarki da yariman Wales wuri ɗaya a taro ba - kuma wannan ya kasance wata babbar alama ta miƙa ragamar. Sarkin ya kasance babban jami'in soji tsawon shekara 32 kuma a yanzu, babban ɗansa Yarima William ya gaje shi. Sarkin ya gana da Yarima William a bikin ba shi muƙamin na soji, bayan da ya sauka daga helikwafta a Hampshire. A wani jawabi da ya yi, Sarkin ya ce ya miƙa ragamar ne "cike da rashin jin daɗi bayan shekara 32 da sanin dukkanku". Ya yi magana kan sha'awar da yake da ita ga aikin rundunar sojin sama a Iraq da Afghanistan sannan ya zaɓi babban ɗansa kuma magajinsa. "Ina fatan za ku ci gaba da samun nasara a nan gaba tare da Yariman Wales a matsayin shugabanku. Babban abin shi ne ya iya tuƙa jirgi. Don haka abin ...

Da Dumi-Dumi: NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano

Image
Da Dumi-Dumi: Hukumar NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano Kan Ƙarin Ƙuɗin Wutar Lantarki. Ƙungiyar ƙwadago (NLC) ta ƙasa reshen jihar Kano ta gudanar da wata zazzafar zanga-zanga da safiyar yau Litinin a ofishin kamfanin rarraba wutar lantarki na KEDCO da kuma ofishin hukumar kula da wutar lantarki ta ƙasa (NERC) da ke Kano. Sakataren NLC na jihar, Abbas Ibrahim, ya bayyana cewa; wannan matakin da suka dauka na zanga-zangar ya biyo bayan ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi, wanda ƙungiyar ba za ta lamunta ba. Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Na Zanga-zanga Kan Ƙarin Ƙudin Wutar Lantarki A Nijeriya Karancin Wuta: Nijeriya Za Ta Daina Sayar Wa Kasashen Ketare Wutar Lantarki Ibrahim ya ce; ana gudanar da wannan zanga-zangar ne a duk jahohin Nijeriya baki ɗaya domin neman lallai a janye wannan ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi, tare da mayar da farashin wutar kamar yadda yake a baya. Sai dai kuma kamfanin na KEDCO har yanzu babu wata sanarwa ko martani da ya yi kan zanga-zanga...